No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ana zargin kwamandan Hisbah a Kano da karɓar cin hancin Naira Dubu 50

Daga Jameel Lawan Yakasai

Wata mai ta bawa Kwamandan Hisbah a ƙaramar hukumar Minjibir dake Kano cin hancin kuɗi, kimannin Naira Dubu Hamsin sakamakon kamata da hukumar ta yi da zargin laifin tara Maza da Mata a gidan ta.

Sai dai kwamandan Hisban Malam Abdullahi kyauta ya hau teburin naƙi kan da’awar matar na karɓar cin hanci domin gudanar da waɗancan taruka.

KU KUMA KARANTA: Hisbah a Kano ta ja kunnen Amare da su daina zaman Majalisa idan mazajen su sun fita

‎Matar mai suna Hajiya yabi dake zaune a unguwar yamma a ƙaramar hukumar Minjibir ta aikewa da kwamandan Hisban mai suna Abdullahi kyauta turmin Atamfa da kudi naira dubu hamsin domin ya sahale mata gudanar da tarukan da suka saɓawa Shari’ar musulunci.

‎Tuni dai rundunar ta hisbah a ƙaramar hukumar ta Minjibir ta dukufa domin kauda ɓarnar da wannan hajiya ke tafkawa a yankin.

‎Wannan kuma na zuwa yayin da Al’ummar yankin ke Allah wadai ga irin ta’asar da hajiyar ke haifarwa a garin, inda suka zargi wasu da ba a kai ga gano ko su waye ba ke dafawa hajiya Yabi.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...