No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wata malama, Aderonke Makonde, a ranar Larabar da ta gabata, an maka ta a wata kotun majistire da ke Ikeja a birnin Legas bisa laifin cin zarafin wata ɗalibar makaranta ‘yar shekara tara.

Rundunar ‘yan sandan ta gurfanar da Makonde, mai shekaru 35, malama a makarantar Westgate Land Emperial Creche Nursery and Primary School, Mushin, Legas da laifin cin zarafin ɗaliba.

Sai dai matar ta musanta zargin da ake mata. Lauyan masu shigar da ƙara, DSP Kehinde Ajayi, ya shaida wa kotun cewa Makonde ta ci zarafin ɗalibar ne ta hanyar “tsula mata bulala a jikinta ba tare da tausayi ba tare da yi mata rauni a jiki”.

KU KUMA KARANTA: An maka magini a kotu, bisa laifin satar buhunan siminti 50

Ta ce laifin ɗalibar shi ne tana surutu a cikin aji. Ajayi ta ce laifin malamar ya saɓa wa tanadin sashe na 172 na dokar laifuka ta Legas, 2015.

Alƙalin kotun, E. Kubeinje, ya shigar da ƙarar wanda ake tuhumar da bayar da belinsa a kan kuɗi naira 50,000 tare da tsayayyu biyu kowannen su tare da shaidar biyan haraji da kuma tantance adireshinsa.

Daga baya Misis Kubeinje ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 7 ga watan Yuni domin sauraren ƙarar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...