No menu items!

Sample Page Title

Date:

Nan da watanni 2 gwamnonin jihohin Rivers, Filato, Kano da Bayelsa za su koma APC — Arodiogbu

Daga Jameel Lawan Yakasai

Mataimakin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa (yankin kudu maso gabas), Ijeoma Arodiogbu, ya bayyana cewa gwamnonin jihohin Bayelsa, Rivers, Plateau da Kano za su sauya sheka zuwa jam’iyyar mai mulki cikin watanni biyu masu zuwa.

A wata hira da jaridar Punch, Arodiogbu ya ce shirin sauya shekar ba zato ba ne ko jita-jita, illa dai wani abu da zai faru nan ba da jimawa ba.

Ya kara da cewa jam’iyyar APC ba ta rufe kofa ga yiwuwar Gwamna Peter Mbah na Enugu da takwaransa Alex Otti na Abia su ma su koma APC ba.

KU KUMA KARANTA: Namadi Sambo ya ƙaryata komawarsa jam’iyar APC

“Ina magana ne akan gwamnonin Bayelsa, Rivers, Plateau, Kano, ko dai Abia ko Enugu. Cikin watanni biyu masu zuwa, za ku ga sun shiga jam’iyyarmu a hukumance,” in ji shi.

“A bayyane yake cewa Bayelsa na cikin lissafin nan — shi yasa na ambace ta. Game da Adeleke (Gwamnan Osun), ba zan iya bayar da tabbaci ba, amma na san yana ta yin wasu yunkuri.”

Arodiogbu ya ce ‘yan siyasar adawa da ke kokarin hada kawancen jam’iyyun adawa domin fuskantar zaben 2027, burinsu kawai shi ne su fito a kafafen yada labarai, ba don mulki ko ci gaban kasa ba.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...