No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsohuwar Editar Neptune Prime Amina Alhassan ta rasu

Tsohuwar ‘yar jarida kuma tsohuwar edita, sannan babbar jami’i gudanarwa ta jaridar Neptune Prime, Hajiya Amina Alhassan, ta rasu. Ta rasu ne a ranar Talata a wani asibitin daji dake Legas bayan ta yi fama da cutar kansar Mama.

Wani ɗan’uwa, Ahmad Makama, ya fitar da labarin rasuwar ta a shafinsa na Facebook a ranar Talata, 20 ga Mayu, 2025.

KU KUMA KARANTA:Mawallafin Neptune Prime zai ƙaddamar da asibitin cutar kansa, makaranta, da gidauniyar tallafi a Yobe

Amina, ‘yar tsohon jami’in Diflomasiyya, Ambasada Yahya Alhassan, an haife ta ne a ranar 27 ga Janairu, 1969, kuma ‘yar asalin Jihar Neja ce. Ita tsohuwar ɗaliba ce a Kwalejin ’Yan mata ta Gwamnatin Tarayya da ke Bida, kuma ta yi karatu a Kuwait English School, Jami’ar Maiduguri, da Jami’ar Abuja.

Hajiya Amina ta yi shekaru masu yawa a harkar yaɗa labarai, tsohuwar editan Neptune Prime, wacce daga baya ta zama Babban Jami’in Kula da Kafafen Yada Labarai. Ta yi murabus ne a shekarar 2023 bayan wata ganawa da gwamnatin jihar Neja.

Amina kuma ta kasance tsohuwar Edita ta ƙarshen mako a jaridar LEADERSHIP kuma mamba a Hukumar Edita.

Za a yi jana’izar ta a yau (Laraba) da ƙarfe 2 na rana, bayan sallar Azahar a babban masallacin Abuja. Ta rasu tana da shekaru 56, ta bar ‘ya’ya huɗu, uwa da sauran ‘yan’uwa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...