No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙasashen duniya sun yi ƙira ga Isra’ila da ta taƙaita ayyukanta a birnin Rafah da ke kan iyaka da kudancin ƙasar, inda miliyoyin ‘yan gudun hijira suka fake.

Wani hari ta sama da Isra’ila ta kai kan wani gida a birnin Gaza da ke kudancin ƙasar ya kashe aƙalla mutane 9, shida daga cikinsu yara ne, a cewar hukumomin asibitin yankin a ranar Asabar, wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kusan tsawon watanni bakwai a yankin na Falasɗinawa da ta yi wa ƙawanya.

Yaƙin da Isra’ila ke yi da ƙungiyar mayaƙan Hamas ya haddasa fargaba a yankin gabas ta tsakiya da ke fama da rikice-rikice.

KU KUMA KARANTA:Iran ta kai hari mafi muni kan Isra’ila

Harin da aka kai da yammacin ranar Juma’a ya shafi wani gini da ke yammacin yankin Tel Sultan a birnin Rafah, a cewar jami’an tsaron farin kaya na Gaza. An kai gawarwakin yaran shida, da mata biyu da namiji ɗaya zuwa asibitin Abu Yousef al-Najjar da ke Rafah, kamar yadda bayanan asibitin suka nuna.

A asibitin ‘yan uwan mamatan sun yi ta kuka tare da rungumar gawarwakin yaran, da aka naɗe da farin ƙyalle, yayin da wasu suka yi ta jajanta musu.

A yayin wani taron manema labarai ranar Juma’a, a wurin taron ƙungiyar ƙasashen G-7 da aka yi a ƙasar Italiya, Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya faɗi cewa gwamnatin Biden “ba za ta goyi bayan wani gagarumin farmakin soja a Rafah ba.”

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...