No menu items!

Sample Page Title

Date:

EFCC ta sake buɗe shari’ar zargin Rabi’u Kwankwaso, Ayodele Fayose da wasu tsaffin gwamnoni 11 da ke damfarar sama da N772bn.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta kuma miƙa wa wasu tsofaffin Ministoci kuma a halin yanzu tana binciken N81.6bn da ake zargin an wawure a ma’aikatar agaji da yaƙi da fatara.

A ranar Lahadin nan ne hukumar tace wasu dala biliyan 2.2 na nufin siyan makamai domin tallafawa yaƙin da ake yi da ‘yan ta’adda amma waɗanda ake zargin sun ɓatar da su ta hanyar karkatar da kuɗaɗen tare da tsohon mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Sambo Dasuki; marigayi ɗan jarida, Raymond Dokpesi, tsohon gwamnan jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa; da tsohon ƙaramin ministan kudi, Bashir Yuguda da dai sauransu.

Yayin da Dasuki ke tsare a hannun jami’an tsaro na farin kaya a shekarar 2015, EFCC ta kama Dokpesi, Bafarawa, Yuguda da sauransu.

KU KUMA KARANTA: EFCC ta gurfanar da tsohon ministan lantarki, Olu Agunloye

An kama su ne bayan da kwamitin shugaban ƙasa da ya binciki sayan makamai a zamanin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya tuhume su.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...