Kotu ta yanke wa sojan da ya kashe Sheikh Goni Aisami hukuncin kisa

0
142

Kotu a Jihar Yobe ta yanke wa sojan da ya kashe Sheikh Goni Aisami hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Kotun wadda ke zama a Potiskum ta yanke hukuncin ne a ranar talata bayan ta samu Lance Corporal John Gabriel da laifin kisan malamin.

Mai Shari’a Usman Zanna Mohammed ne ya sanar da hukuncin kisan kan Gabriel wanda a baya ke ƙarƙashin Bataliya ta 241 da ke Nguru.

Sannan kuma alkalin kotun ya yanke wa Lance Corporal Adamu Gideon hukuncin ɗaurin shekara goma a gidan yari sakamakon samunsa da laifin haɗin baki.

Kotun ta ce ta yanke wannan hukuncin ne bayan ta yi dogon nazari kan irin hujjojin da aka gabatar a gabanta waɗanda suka gamsar da ita.

KU KUMA KARANTA: Yadda Sheikh Bagoni Aisam Gashuwa ya rasu

Sojojin da aka kama da laifin sun kashe fitaccen malamin ne bayan ya rage musu hanya da motarsa kan hanyar Kano zuwa Gashuwa.

Sheikh Goni Aisami fitaccen malami ne ɗan asalin garin Gashuwa a Jihar Yobe da ke arewa maso gabashin Najeriya.

Kafin rasuwarsa, Sheikh Goni Aisami fitaccen malamin Addinin Musulunci ne daga garin Gashuwa na Jihar Yobe wanda yake gudanar da tafsirin Al-Ƙur’ani a fadar Sarkin Gashuwa da kuma sauran wurare.

Leave a Reply