No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmad Umaru Fintiri, ya jagoranci shugabannin ƙungiyar Izala wajen kai wa takwaransa na Bauchi Gwamna Bala Mohammad ziyara game da taƙaddamar Shaikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi.

Gwamna Fintiri ya wallafa a shafinsa na Tuwita cewa shi da Shaikh Abdullahi Bala Lau da Shaikh Kabiru Gombe da kuma Shaikh Abdulwahab Kano sun kai ziyarar a ƙoƙarin “kawo ƙarshen shari’ar da ake yi wa Shaikh Dutsen Tanshi”.

“Ina matuƙar godiya ga Gwamna Bala Mohammed bisa fahimtarsa ​​da hikimarsa wajen ji daga dukkan ɓangarorin da abin ya shafa, da manufar samar da zaman lafiya,” in ji Fintiri.

KU KUMA KARANTA: Kotu ta ba da belin Dakta Idris Dutsen Tanshi bisa sharaɗi

A nasa ɓangaren, Gwamna Bala Muhammad ya bayyana cewa addini abu ne mai sammatsi da ya kamata mutane su kula.

Ya kuma yaba wa malaman bisa fahimtarsa da kuma Dakta Idris Abdul’aziz da suka yi.

A baya-bayan nan ne aka sako fitaccen malamin, Shaikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi daga gidan yari, bayan ya shafe tsawon kwanaki a wata ƙara da ta shafi zargin aikata saɓo da ake yi masa, na kalaman ɓatanci da rashin ɗa’a da ya yi akan fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...