No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa, (EFCC), ofishin shiyyar Ibadan, ta cafke wani ma’aikacin Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya, (FMC) Idi-Aba, Abeokuta a Ogun, da wasu mutane 47 bisa zarginsu da hannu a damfara ta yanar gizo.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Wilson Uwujaren ya sanya wa hannu kuma aka bai wa manema labarai ranar Juma’a a Ibadan.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya bayar da rahoton cewa, an kama mutane 48 da ake zargi a Ogun da uku a jihar Oyo.

KU KUMA KARANTA: Shugaba Tinubu ya dakatar da shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa

Uwujaren ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a ranar Laraba a unguwar Idi-Aba da ke Abeokuta, biyo bayan samun bayanan sirri da ake zarginsu da aikatawa.

Ya ce kayayyakin da aka ƙwato daga hannun waɗanda ake zargin sun haɗa da wasu manyan motoci guda bakwai, wayoyin hannu da dama, kwamfutar tafi-da-gidanka, da agogon hannu na apple da dai sauransu.

Uwujaren ya ce an kama wasu mutane biyu a rana guda a unguwar Idi-Igba da ke Ibadan a jihar Oyo, kuma an ƙwato musu motoci biyu da wasu kayayyaki masu daraja a hannunsu.

Ya ce rundunar ‘yan sandan Najeriya ta jihar Oyo ta kuma kama wani da ake zargi da aikata laifuka ta yanar gizo ga hukumar EFCC.

Uwujaren ya ce an kama wanda ake zargin ne a gidansa bisa zarginsa da hannu a ayyukan damfara. Ya ce an ƙwato masa mota ƙirar Honda Civic da wayoyin hannu.

Mista Uwujaren ya ce za a gurfanar da dukkan waɗanda ake zargin a gaban kotu bayan an kammala bincike.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...