No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga; Isah Ahmed, Jos.

KUNGIYAR nan ta Haske da ke garin Jos, babban birnin Jihar Filato, da ke tallafawa marayu da gajiyayyu, ta tallafawa marayu maza da mata da gajiyayyu guda 764, da kayan Sallah. Shugabar Kungiyar, Hajiya Maryam Shehu Nabage ce, ta bayyana haka a lokacin da take zantawa da wakilinmu.

Ta ce duk da yadda shekarar bana ta kasance na halin matsi, sun yi kokarin rabawa marayu da gajiyayyu guda 764, tufafin sallah a wurare daban daban na ciki da wajen Najeriya.

Ta ce wuraren da suka raba kayan, sun hada da nan Jos da jihohin Bauchi da Kano da Kaduna da Katsina da Jam’horiyar Nijar.

Ta ce kayan da suka raba, sun hada da yadudduka da shaddoji da Atamfofi da takalmin silifa kafa 220.

Hajiya Maryam ta yi bayanin cewa kan maganar ciyarwa kuwa, kamar yadda suka saba a duk lokacin Azumi, a bana ma kullum suna tuka tuwon shinkafa da tuwon masara suna rabawa marayu, tun farkon Azumi har karshen Azumin.

Ta yi kira ga masu hali, su taimaka masu kan wannan aiki da suka sanya a gaba.

admin
adminhttps://neptuneprimehausa.com
Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...