Connect with us

'Yan bindiga

Ƴan bindigar da suka sace ɗalibai 286 sun buƙaci kuɗin fansa naira biliyan ɗaya

Published

on

Ƴan bindiga da suka yi garkuwa da ɗalibai da ma’aikata 286 a wata makaranta a arewacin Najeriya a makon da ya gabata, sun buƙaci a ba su Naira biliyan ɗaya, kwatankwacin dala 620,432 a matsayin kuɗin fansa, kamar yadda kansilan yankin kuma mai magana da yawun iyalan wadanda aka yi garkuwa da su ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

A ranar 7 ga watan Maris ne aka sace yara ƴan makarantar da ma wasu manyan ɗalibai da kuma wasu ma’aikatan makarantar a garin Kuriga da ke jihar Kaduna a arewa maso yammacin Najeriya, a karon farko da aka yi garkuwa da mutane da dama irin haka tun shekara ta 2021.

Kansilan, Jubril Aminu, wanda kuma shi iyalan waɗanda aka yi garkuwa da su suka zaɓa ya dinga magana a madadinsu, ya ce masu garkuwan sun ƙira shi ta wayar tarho ranar Talata.

“Sun buƙaci a biya su biya jimillar naira biliyan ɗaya a matsayin kuɗin fansa ga ɗaukacin ɗalibai da ma’aikatan makarantar,” in ji Aminu.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun sace ‘yan makarantar Allo a Sakkwato

“Sun ba da wa’adin biyan kuɗin fansa cikin kwanaki 20, daga ranar da aka yi garkuwa da su, sun ce za su kashe dukkan ɗaliban da ma’aikata idan har ba a biya kuɗin fansar ba.”

Shi ma Idris Ibrahim, wani zaɓaɓɓen jami’i a karamar hukumar Kuriga, ya tabbatar da batun buƙatar kuɗin fansa da adadin kuɗin.

“E, masu garkuwa da mutane sun ƙira al’ummar ta lambar Jubril Aminu, suka kuma gabatar da buƙatar,” in ji shi.

Ibrahim ya shaida wa Reuters cewa, “Sun kira ne daga wata ɓoyayyiyar lamba amma hukumomi na aiki don gano lambar.”

Ya ƙara da cewa jami’an tsaro na ɗaukar ƙwararan matakai domin ganin an sako ɗaliban.

Reuters ya ruwaito cewa Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Kaduna Samuel Aruwan, bai amsa saƙon da ta aika masa ta son jin ta bakinsa ba game da buƙatar masu garkuwa da mutane.

Haka shi ma mai magana da yawun Shugaba Tinubu bai amsa buƙatar son jin ta bakinsa ba.

Sai dai, Ministan yaɗa labaran kasar, Mohammed Idris, ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba cewa, matsayar Tinubu kan sace-sacen da aka yi a Kuriga shi ne jami’an tsaro su tabbatar da sako mutanen da aka yi garkuwa da su ba tare da biyan masu garkuwa da mutanen ba.

“Shugaban ƙasa ya ba da umarnin cewa dole ne jami’an tsaro cikin gaggawa su tabbatar da cewa an dawo da waɗannan yaran da duk waɗanda aka yi garkuwa da su lafiya, sannan kuma su tabbatar ba a biya ko sisin kwabo domin kuɗin fansa ba.”

Gwamnatin da ta gabata ta Muhammadu Buhari ta kafa dokar hana biyan kuɗin fansa inda ta ce za a ɗaure duk wanda aka samu ya biya kuɗin fansa don a sako wani nasa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

Published

on

'Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

‘Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

Wata ƙungiya ɗauke da makamai ta kai hari a yayin wani bikin aure a tsakiyar ƙasar Mali tare da kashe aƙalla mutane 21, kamar yadda mazauna yankin suka faɗa a ranar Laraba.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da shugabannin sojojin ƙasar Afirka ta Yamma ke fafutukar yaƙi da tashe-tashen hankula daga masu tsattsauran ra’ayi.

Maharan sun kutsa ƙauyen Djiguibombo akan babura wanda ke garin Bandiagara a yammacin ranar Litinin ɗin da ta gabata yayin da mazauna yankin ke bikin ma’auratan, a cewar Bakary Guindo, shugaban ƙungiyar matasan yankin.

KU KUMA KARANTA:‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

“Yawancin waɗanda abin ya shafa yankan rago aka musu” in ji Guindo.

Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin, sai dai ya biyo bayan irin wanda ƙungiyar masu tsattsauran ra’ayi ta JNIM da ke da alaƙa da Al-Qaida ke kai hare-hare a yankin.

Continue Reading

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

'Yan bindiga

Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Published

on

‘Yan bindigar dai sun aukawa jami’ar kimiyya da fasaha ne dake garin Osara a ƙaramar hukumar Adabi a jihar Kogi inda bayan jikkata wasu ɗaliban, sannan suka yi garkuwa da wasu kimanin 57.

Malam Ɗan Asabe wani mazaunin jihar Kogi yace ‘yan bindigar sun haura cikin jami’ar ne ta baya suka dinga harbin kan mai uwa da wabi kamar yadda ya yiwa wakilin Muryar Amurka bayani ta wayar salula.

Tuni dai Gwamnatin jihar Kogin ta yi Allah wadai da wannan hari tare da nuna takaicinta akan lamarin.

Kwamishinan Labarai na jihar Kogin, Kensly Fanwo, yace, kawo yanzu ba su tantance adadin ɗaliban da ‘yan bindigar suka sace ba, amma sun haɗa hannu da jami’an tsaro domin ganin an kuɓuta da ɗaliban cikin ƙoshin lafiya.

KU KUMA KARANTA:’Yan bindiga sun sace ɗalibai a Jami’ar Jihar Kogi

Ya ƙara da cewa, a lokacin da gwamnatin jihar ta samu labarin ta yi ƙoƙarin jibga jami’an tsaro a wannan yanki domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A wata sanarwa daga kakakin ‘yan sandan jihar Kogin, Wilyans Aya, ya ce kwamishinan ‘yan sandan ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban.

Garkuwa da ɗaliban makaranta dai na ci gaba da ɗaukar hankali a Nijeriya, al’amarin da masana suka ce babbar barazana ce a ɓangaren Ilimi a ƙasar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like