No menu items!

Sample Page Title

Date:

Zan yi haɗaka da sabuwar jam’iyyar ADC don a kayar da Tinubu, amma ba zan fice daga jam’iyar PDP ba – Sule Lamiɗo

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamiɗo ya bayyana haka ne a hirarsa da gidan Rediyon BBC Hausa a ranar Asabar.

Lamiɗo ya ce yadda ya san halin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a kan cika burin da ya sa a gaba, na cikin abubuwan da suka ƙara masa ƙaimi wajen shiga sabuwar haɗakar jam’iyyar ‘yan hamayya ta ADC.

KU KUMA KARANTA: Jagoran PDP a Yobe, Adamu Waziri ya fice daga jam’iyar ya koma ADC

Ya ce, ya amince ya yi aiki da haɗakar ne a wani yunƙuri na kawar da gwamnatin Tinubun a babban zaɓen ƙasar mai zuwa a 2027.

Sai dai a ɓangare guda Sule Lamiɗo, ya ce ba zai fita daga jam’iyyarsa ta PDP ba, hakan wani salo ne da ke ƙoƙarin zame wa ruwan dare a siyasar Najeriyar a baya-bayan nan.

A zantawarsa da wakilinmu na Kano, Zahraddeen Lawan cikin filinmu na Gane Mini Hanya a wannan mako, tsohon gwamnan Jigawa ya fara ne da yin waiwaye kan abin da yake gani shi ne mafari na halin da siyasar Nijeriya ta samu kanta ciki.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...