Connect with us

Labarai

Za a gurfanar da mutanen da ake zargi da rajin kafa ƙasar Yarbawa a kotu – Ƴan sanda

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Oyo da ke kudancin Najeriya ta ce nan gaba kaɗan za ta gurfanar da mutanen da ta kama bisa zargin fafutukar kafa ƙasar Yarbawa a gaban kotu.

A ranar Asabar da ta wuce ne, ƴan sanda suka kama ƴan kungiyar bayan mamayar da suka yi wa Ofishin gwamnar jihar Oyo da kuma majalisar dokokin jihar suna sanye da kakin soji kuma riƙe makamai daban-daban da kuma tutar ƙasar da suke son kafawa.

Kazalika rahotanni sun ce mutanen sun yi yunƙurin kutsa kai cikin ofishin gwamnan jihar, amma jami’an tsaro su fatattake su tare da kama da dama daga cikinsu.

Ana zargin matar hamshakin ɗan kasuwa kuma fitaccen ɗan siyasa, marigayi Cif Moshood Abiola, mai suna Dupe Onitiri- Abiola da ɗaukar nauyin masu fafutukar bayan wani bidiyo da ta wallafa wanda ya karaɗe shafukan intanet, tana mai iƙirarin ɓallewa daga Najeriya da kuma kafa shugabancin ƙasa ga al’ummar Yarbawa.

KU KUMA KARANTA: Rashin tsaro: Gwamnoni 16 na goyon bayan kafa ‘yan sandan jihohi

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Oyo, Hamzat Adebola, ya bayyana lamarin a matsayin laifi da rashin kishi da cin amanar ƙasa da kuma ayyukan ta’addanci a yayin da yake gabatar da mutanen da ake zargi a gaban ‘yan jarida, yana mai cewa ”za a hukunta su bisa tanadin doka.”

“Da farko ƴan sanda sun gargaɗi masu fafutukar da su watse amma sai suka yi kunnen-ƙashi daga nan gangaminsu ya juya zuwa rikici sai suka buɗe wuta kan ‘yan sanda da kuma tawagar jami’an sa-kai na Amotekun da ke wurin,” a cewar kwamishinan.

”An ƙwato bindigogi masu sarrafa kansu guda biyar da wasu tarin makamai da kayan sojoji guda 72 da harsashai 405 da dai sauransu,” in ji Kwamishinan ƴan sandan.

Haka kuma jaridun Najeriya sun ruwaito cewa ƴan sandan jihar Oyo na neman Onitiri-Abiola ruwa-a-jallo, sai dai a yayin jawabin Kwamishinan bai ambaci sunanta ba amma mai bai wa Gwamnan Jihar Oyo shawara kan harkokin tsaro Mista Fatai Owoseni ya ce ana sane da cewa ita ce take jagorantar ƙungiyar ta masu rajin kafa ƙasar Yarbawa daga Najeriya.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Oyo ya ce rundunar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da haɗin kan Najeriya.

“Ina so na yi amfani da wannan dama wajen tunatar da masu aikata laifuka cewa jihar Oyo jiha mai karɓar baki da kuma haziƙan mutane waɗanda ke alfahari da kansu a fannin ƙirƙire-ƙirƙire, da kuma aiki tuƙuru da wadata,” in ji shi.

Wasu daga cikin waɗanda aka kama sun shaida wa manema labarai cewa ba su yi nadamar mamayar da suka yi wa Ofishin gwamnatin jihar ba.

Sun ce sun bi matakai da suka kamata kuma ba su ci amanar ƙasa ba. “Ba mu yi nadama ba, mun bi tsarin da ya kamata mu bi,” kamar yadda suka shaida wa manena labarai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like