No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sanda a Ebonyi, ta tabbatar da cewa Rev. Fr. Joseph Azubuike da aka yi garkuwa da shi a ranar Litinin, ya samu ‘yanci.

Wata sanarwa ranar Talata a Abakaliki ta hannun SP Onome Onovwakpoyeya, mai magana da yawun rundunar, ta ce an sako Mista Azubuike ba tare da wani rauni ba.

An yi garkuwa da malamin ne tare da wasu mutane uku a garin Isu da ke ƙaramar hukumar Onicha ta jihar.

KU KUMA KARANTA: Wasu ‘yan bindiga sun kashe ma’aikacin INEC, sun sace matarsa a Ebonyi

An sake Mista Azubuike, wani limamin cocin St. Charles Parish, Mgbaleze Isu a ƙaramar hukumar Onicha, da misalin ƙarfe 18:00pm.

“Rabaran. An kuɓutar da Baba Joseph Azubuike ba tare da jin rauni ba, ko wani tashin hankali sakamakon haɗin gwiwa da jami’an rundunar suka yi.

“Ana ci gaba da farautar waɗanda suka aikata laifin, waɗanda suka tsere a lokacin aikin ceto. Rabaran, mahaifin yana asibiti yanzu don duba lafiyarsa,” in ji kakakin ‘yan sandan.

Shima a cikin wata sanarwa, Rabaran Father Mathew Opoke, Chancellor na Abakaliki Diocese ya tabbatar da ceto Azubuike a ranar talata.

Ya ce sauran ukun da aka kama, masu garkuwar sun sako su ba tare da wani sharaɗi ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...