No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da shugaban ƙaramar hukumar Akwanga a jihar Nasarawa Safiyanu Isah.

An yi garkuwa da Isah ne a daren Litinin, 1 ga watan Janairu, 2024, a ƙauyen Ningo, dake kan titin Akwanga-Andaha.

Mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Kamal Dauda Rija, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar, ya ce an sace shi ne tare da wasu, ciki har da wani fitaccen mai bayar da agaji a ƙaramar hukumar, Adamu Umar, wanda aka fi sani da Macciɗo.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe wasu mutane a Nijar

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Ramhan Nansel, da jami’an tsaro da suka haɗa da ‘yan sanda da sauran hukumomi, sun yi gaggawar fara farautar waɗanda suka yi garkuwa da su domin ganin an sako waɗanda aka sace.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...