Connect with us

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun sace mata biyar da suka tafi biki a Katsina

Published

on

A ƙalla mutane huɗu ciki har da ɗan sanda guda ɗaya ne aka kashe yayin da aka yi awon gaba da wasu da dama a lokacin da ‘yan ta’adda suka kai hari a Domawa a ƙaramar hukumar Ɗanmusa ta Jihar Katsina a daren ranar Alhamis. 

An kuma sace wasu ‘yan mata biyar da wani mutum ɗaya a wani hari na daban da aka kai Sukola, da ke ƙaramar hukumar Bakori a jihar. 

Jaridar Premium Times ta ambato wata majiya na cewa ‘yan ta’addan sun kai hari a cikin ƙauyen na Domawa ne ‘yan mintuna kaɗan bayan ƙarfe 9:00 na dare. 

“Yan ta’addan sun shiga cikin ƙauyen inda suka fara harbi ba ƙaƙƙautawa domin tsoratar da mutane. 

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga na bautar da mutane a jihar Katsina

Mutum ukun da ‘yan ta’addan suka kashe, ‘yan ta’addan sun ɗauke su a matsayin barazana, domin a lokacin da (‘yan ta’addan) suka ce su bi su, sai suka ƙi.” 

Ya bayyana sunayen waɗanda aka kashe a matsayin Sa’idu Mai Kyaran, Na Doguwa da Suyudi Mai Tabarma yayin ya ce sunan ɗan sandan Hassan.

A yankin kudancin jihar Katsina, ‘yan ta’addan sun kai wani hari da ya kai ga yin garkuwa da wasu ‘yan mata biyar da suke halartar wani bikin ɗaurin aure a ƙauyen Sukola.

Wani shugaban matasa a ƙauyen da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa “Su (‘yan matan) sun fito ne daga ƙauyuka daban-daban da ke kewayen Sukola. 

Sun je ƙauye ne domin taya murna ga wata ƙawarsu da za a yi bikinta a ranar Asabar. 

Kun san mata suna da shagulgulan da suke kafin ɗaurin aure, bayan an tashi shagalin dare ne ‘yan ta’adda suka far wa ƙauyen.” 

Ya bayyana sunayen ‘yan matan da aka sace matsayin Maryam Sani, Maijidda Kabir, Abida Matthew da Maryam Ibrahim. 

Ya ce bai san sunan ta ƙarshen su ba. A yayin harin da aka kai da misalin ƙarfe 11:00 na dare, majiyar ya ce ‘yan ta’addan sun zo ne da “makamai da dama,” inda suka toshe duk wata hanyar shiga cikin ƙauyen tare da ci gaba da harbe-harbe domin haifar da ruɗani. 

Legit Hausa ta tuntubi muƙaddashin kakakin rundunar ‘yan sanda jihar Katsina, Abubakar Sadiq, domin samun ƙarin bayani kan ƙoƙarin da ake wajen ceto ‘yan matan, bai dawo da saƙon da aka tura masa ba har zuwa lokacin kammala haɗa wannan rahoton.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

'Yan bindiga

Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Published

on

‘Yan bindigar dai sun aukawa jami’ar kimiyya da fasaha ne dake garin Osara a ƙaramar hukumar Adabi a jihar Kogi inda bayan jikkata wasu ɗaliban, sannan suka yi garkuwa da wasu kimanin 57.

Malam Ɗan Asabe wani mazaunin jihar Kogi yace ‘yan bindigar sun haura cikin jami’ar ne ta baya suka dinga harbin kan mai uwa da wabi kamar yadda ya yiwa wakilin Muryar Amurka bayani ta wayar salula.

Tuni dai Gwamnatin jihar Kogin ta yi Allah wadai da wannan hari tare da nuna takaicinta akan lamarin.

Kwamishinan Labarai na jihar Kogin, Kensly Fanwo, yace, kawo yanzu ba su tantance adadin ɗaliban da ‘yan bindigar suka sace ba, amma sun haɗa hannu da jami’an tsaro domin ganin an kuɓuta da ɗaliban cikin ƙoshin lafiya.

KU KUMA KARANTA:’Yan bindiga sun sace ɗalibai a Jami’ar Jihar Kogi

Ya ƙara da cewa, a lokacin da gwamnatin jihar ta samu labarin ta yi ƙoƙarin jibga jami’an tsaro a wannan yanki domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A wata sanarwa daga kakakin ‘yan sandan jihar Kogin, Wilyans Aya, ya ce kwamishinan ‘yan sandan ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban.

Garkuwa da ɗaliban makaranta dai na ci gaba da ɗaukar hankali a Nijeriya, al’amarin da masana suka ce babbar barazana ce a ɓangaren Ilimi a ƙasar.

Continue Reading

'Yan bindiga

An sace limaman coci 6 a Anambara

Published

on

Rahotanni daga Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu limaman Coci shida yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa birnin Awka na jihar Anambara a kudu maso gabashin Najeriya.

Bayanai sun yi nuni da cewa ‘yan bindigar sun sace Archbishop Uka Uka na Mujami’ar Brotherhood of the Cross and Star, (BCS) da matarsa Anne Osim da ɗansu Ronald Uka Osim.

Sauran limaman Cocin sun haɗa da Azuka Ochu, Moses Okafor da Anderson Akwazie a cewar jaridar Daily Trust.

Jaridar Daily Post ta yanar gizo ta ruwaito cewa mutanen na hanyarsu ta zuwa Awka ne daga jihar Abiya don gudanar da ayyukan wa’azi a lokacin da lamarin ya faru.

Al’amarin ya faru ne a ranar 1 ga watan nan na Mayu kamar yadda rahotanni suka nuna.

KU KUMA KARANTA:An halaka direba da sace mutum 2 a hanyar Abuja

“Mun damu matuƙa, amma muna da tabbacin cewa Ubangijin da suke bautawa zai taimaka musu.” Jaridar ta Daily Post ta ruwaito wani Limami a Cocin ta BCS, Bishop Denis Onuoha yana cewa.

Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar Anambara, ta ce ba ta da masaniyar aukuwar wannan al’amari.

“Ba mu da wasu bayanai da suka nuna aukuwar wannan al’amari a jihar Anambara.” Wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce a ranar Asabar ɗauke da sa hannun Kakakinta SP Tochukwu Ikenga.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “muna ƙira ga jama’a da su taimaka mana da bayanai kan wannan al’amari idan har ya faru, hakan zai ba mu dama mu ƙaddamar da bincike.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like