‘Yan bindiga sun sace ɗaliban jami’ar Jos bakwai

Wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a tantance su waye ba, sun yi garkuwa da ɗaliban jami’ar Jos su bakwai.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alfred Alabo, ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) aukuwar lamarin a ranar Laraba a garin Jos.

A cewar Alabo, an sace ɗaliban ne a ranar Litinin da daddare a masauƙinsu da ke wajen harabar jami’ar.

Ya bayyana cewa an sace ɗaliban ne a lokacin da suke karatun jarabawar zango na biyu, wanda aka fara a ranar Talata.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe Fasto da mutane 20 a Filato

“Gaskiya ne wasu miyagu sun yi awon gaba da ɗalibai bakwai na jami’ar Jos.

“An sace su ranar Litinin da misalin ƙarfe 8:30 na dare a hostel ɗin su, dake kan titin Bauchi ring road a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.

“Kwamishanan ‘yan sandan jihar Bartholomew Onyeka, ya tura jami’an ‘yan sanda ɗauke da makamai domin kamo masu garkuwa da mutane tare da tabbatar da ganin an sako ɗaliban da aka sace.

“Operation Safe Haven (OPSH), da hukumomin tsaro sun kuma tura jami’ansu domin gudanar da bincike da ceto,” inji shi.

Mista Alabo ya shawarci ɗalibai da mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu, yana mai jaddada cewa jami’an tsaro suna bakin ƙoƙarinsu wajen ganin an dawo da ɗaliban da aka sace cikin gaggawa.


Comments

2 responses to “‘Yan bindiga sun sace ɗaliban jami’ar Jos bakwai”

  1. […] KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun sace ɗaliban jami’ar Jos bakwai […]

  2. […] KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun sace ɗaliban jami’ar Jos bakwai […]

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *