Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun kashe basaraken gargajiya da ‘ya’yansa huɗu, sun sace shanu 100 a Kaduna

Published

on

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kashe wani mai riƙe da sarautar gargajiya, mai suna Arɗo na Birni da Kewaye na Masarautar Zazzau, Shuaibu Mohammed tare da ‘ya’yansa huɗu. Lamarin ya faru ne a daren ranar asabar da misalin ƙarfe 10 na dare a ƙauyen Ɗorayi da ke ƙaramar hukumar Zariya a jihar Kaduna.

‘Yan fashin sun kuma yi awon gaba da shanu 100 na mamacin.

Matar marigayin, Malama Halima Shuaibu ta shaida wa manema labarai bayan jana’izar waɗanda aka kashen cewa ‘yan bindigar sun harbe mijinta a kai.

“An fito da Arɗo daga ɗakin kwanansa, aka harbe shi har sau biyu, kuma ya mutu nan take.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe ‘yan uwa biyu a Kaduna

“’Yan bindigar sun bi ɗaki-ɗaki a cikin harabar gidan inda suka kashe ‘ya’yana huɗu da suke da aure da ‘ya’ya.

“Waɗanda aka kashe su ne Adamu Shuaibu, Musa Shuaibu, Abubakar Shuaibu da Ibrahim Haruna.

“Bayan sun kai hari harabar gidan, sun kuma tafi da shanu sama da 100,” in ji ta.

Mutum ɗaya tilo da ya tsira daga harin a cikin yaran Arɗo, Abdurrahman Shuaibu ya ce ‘yan bindigar sun harbe wasu mutane biyu a hanyarsu ta fita daga ƙauyen.

Da aka tuntuɓi Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, DSP Mohammed Jalige, ya ce har yanzu ba a yi masa bayani kan lamarin ba.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: ‘Yan sanda sun kashe ‘yan ta’adda biyar, sun ƙwato dabbobi 143 a Katsina | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Wasu ‘yan bindiga sun kashe ma’aikacin INEC, sun sace matarsa a Ebonyi | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: An sace mahaifar ta, bayan ta haihu a wani Asibiti a Ondo | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like