Connect with us

'Yan bindiga

’Yan bindiga sun kashe ɗan uwan amarya, sun sace mahalarta biki a Kaduna

Published

on

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

’Yan bindiga sun sace gomman mahalarta biki a wani hari da suka kai ƙauyen Gidan Kunkun da ke gundumar Dawaki a ƙaramar hukumar Ƙauru ta Jihar Kaduna.

Wani jami’in tsaron sa-kai ya shaida wa Aminiya cewa an kashe mutum ɗaya lokacin harin da aka kai ana tsaka da shagalin bikin aure.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, matashin da aka kashe mai shekaru 24 ɗan uwan amaryar da ake bikin auren nata ne.

Tuni dai an kai gawarsa ƙaramar hukumar Ikara domin yi masa jana’iza, yayin da mutane ukun da suka jikkata — Iliyasu Ibrahim da Zaphaniya Danbala da Victor Audu — suke samun kulawa a babban asibitin garin Kauru.

Daga cikin waɗanda aka tabbatar cewa ’yan bindigar sun yi awon gaba da su akwai Josia Sama’ila da Adamu Bulus da Enoch Bulus da Enoch Ibrahim da Yahuza Sama’ila da Lawan Francis da wani fasto a cocin Heken da ke ƙauyen na Gidan Kunkun da kuma wasu matan aure kimanin 10 da ’ya’yansu.

KU KUMA KARANTA: Yadda ’yan bindiga suka kashe mutum 4 suka sace 39

Bayanai sun ce ya zuwa yanzu dai fargaba ta lafa yayin da mutanen garin sun koma ci gaba da harkokinsu.

Aminiya ta tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan wanda ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa sun ɗauki matakin ganin cewa sun ƙwato mutanen da aka ɗauke nan ba da daɗewa ba.

Kazalika, ASP Mansir ya yi ƙira ga al’umma da su riƙa sa ido a kan masu kai-komo a yankinsu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

Published

on

'Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

‘Yan bindiga sun kashe mutum 21 a wani bikin aure

Wata ƙungiya ɗauke da makamai ta kai hari a yayin wani bikin aure a tsakiyar ƙasar Mali tare da kashe aƙalla mutane 21, kamar yadda mazauna yankin suka faɗa a ranar Laraba.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da shugabannin sojojin ƙasar Afirka ta Yamma ke fafutukar yaƙi da tashe-tashen hankula daga masu tsattsauran ra’ayi.

Maharan sun kutsa ƙauyen Djiguibombo akan babura wanda ke garin Bandiagara a yammacin ranar Litinin ɗin da ta gabata yayin da mazauna yankin ke bikin ma’auratan, a cewar Bakary Guindo, shugaban ƙungiyar matasan yankin.

KU KUMA KARANTA:‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

“Yawancin waɗanda abin ya shafa yankan rago aka musu” in ji Guindo.

Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai harin, sai dai ya biyo bayan irin wanda ƙungiyar masu tsattsauran ra’ayi ta JNIM da ke da alaƙa da Al-Qaida ke kai hare-hare a yankin.

Continue Reading

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

'Yan bindiga

Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Published

on

‘Yan bindigar dai sun aukawa jami’ar kimiyya da fasaha ne dake garin Osara a ƙaramar hukumar Adabi a jihar Kogi inda bayan jikkata wasu ɗaliban, sannan suka yi garkuwa da wasu kimanin 57.

Malam Ɗan Asabe wani mazaunin jihar Kogi yace ‘yan bindigar sun haura cikin jami’ar ne ta baya suka dinga harbin kan mai uwa da wabi kamar yadda ya yiwa wakilin Muryar Amurka bayani ta wayar salula.

Tuni dai Gwamnatin jihar Kogin ta yi Allah wadai da wannan hari tare da nuna takaicinta akan lamarin.

Kwamishinan Labarai na jihar Kogin, Kensly Fanwo, yace, kawo yanzu ba su tantance adadin ɗaliban da ‘yan bindigar suka sace ba, amma sun haɗa hannu da jami’an tsaro domin ganin an kuɓuta da ɗaliban cikin ƙoshin lafiya.

KU KUMA KARANTA:’Yan bindiga sun sace ɗalibai a Jami’ar Jihar Kogi

Ya ƙara da cewa, a lokacin da gwamnatin jihar ta samu labarin ta yi ƙoƙarin jibga jami’an tsaro a wannan yanki domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A wata sanarwa daga kakakin ‘yan sandan jihar Kogin, Wilyans Aya, ya ce kwamishinan ‘yan sandan ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban.

Garkuwa da ɗaliban makaranta dai na ci gaba da ɗaukar hankali a Nijeriya, al’amarin da masana suka ce babbar barazana ce a ɓangaren Ilimi a ƙasar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like