Connect with us

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kai hari a masallacin Kaduna, sun kashe mutane bakwai

Published

on

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kaduna a ranar asabar ɗin da ta gabata ta tabbatar da kashe mutane bakwai a lokacin da suke gudanar da sallah a wani masallaci da ke ƙauyen Saya-Saya da ke ƙaramar hukumar Ikara.

Mai magana da yawun rundunar, Mansir Hassan, ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya aukuwar lamarin.

Mista Hassan, mataimakin sufeton ‘yan sanda, ya ce “da misalin ƙarfe 8:00 na dare a ranar Juma’a, mun samu labari daga ƙauyen Saya-Saya cewa an kashe mutane shida a lokacin da suke yin sallar Isha’i a wani Masallaci. “

’Yan bindigar kimanin tara ne a kan babura, sun isa wurin suka far wa mutanen da ke cikin Masallacin.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kai hari a Abuja, sun yi awon gaba da wani magidanci

“A wajen, sun harbe mutane shida yayin da suke addu’a a wani masallaci a ƙauyen.”

Malam Hassan ya ce ‘yan bindigar sun kuma koma wani masallaci da ke Tashar Dauda, ​​shi ma a ƙaramar hukumar Ikara, inda suka kashe mutum ɗaya yayin da uku suka samu raunuka.

Ya ce ɓarayin sun tafi da babura huɗu. “Da samun labarin, sai jami’in ‘yan sanda reshen Ikara ya garzaya da jami’an tsaro zuwa wurin da lamarin ya faru.

“A lokacin da mutanenmu suka isa wurin, ‘yan bindigar sun tsere cikin daji kafin isowar jami’an tsaro.

Ya zuwa yanzu, ba a kama wani mutum a wurin da lamarin ya faru ba, amma an ƙwato harsashi biyar na bindiga ƙirar AK49.

Ya ce an miƙa gawarwakin bakwai ga ‘yan uwansu. Daga cikin mutane ukun da suka jikkata, ya ce an kai biyun zuwa babban asibitin Tudun-Wada da ke jihar Kano, yayin da ɗaya ke kwance a babban asibitin Ikara.

Hassan ya ce ‘yan sanda sun ƙara zage damtse wajen cafke waɗanda ake zargin tare da hukunta su.

Ya ƙara da cewa kwamishinan ‘yan sanda, Musa Garba, yana ƙira ga ‘yan ƙasar da su riƙa kai rahoton duk wani abu da ba a saba gani ba da kuma shakku ga hukumomin tsaro mafi kusa domin ɗaukar matakin da ya dace.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: A nemo waɗanda suka kai hari masallacin Ikara – Gwamnatin Kaduna | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yan bindiga

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Published

on

'Yan bindiga sun kashe malamin jami'a a Katsina, sun sace 'ya'yansa

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a a Katsina, sun sace ‘ya’yansa

Rahotanni daga Jihar Katsina  na cewa ‘yan bindiga sun kashe wani malamin Jami’ar Tarayya ta Dutsinma.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da tsakar dare da misalin ƙarfe 1:30 inda ‘yan bindigar suka afka gidan Dakta Tiri Gyan da ke Yarima Quarters a Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
Mai magana da yawun ‘yan sandan  reshen Katsina Abubakar Sadiq ya tabbatar wa kafar watsa labarai ta Channels  da kisan malamin.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun afka gidan malamin jami’ar da makamai daban-daban inda suka yi ta harbi domin tsorata mazauna rukunin gidajen.

Sun kuma bayyana cewa ɓarayin sun sace yara biyu na Dakta Gyan a lokacin da suka kai harin.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Kashe malamin na zuwa ne mako guda bayan kashe mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Ɗanfodiyo da ke Sokoto Farfesa Yusuf Saidu.

An kashe shi a lokacin da yake hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Sokoto.

Continue Reading

'Yan bindiga

Muna ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban jami’ar da ‘yan bindiga suka sace – Gwamnatin Kogi

Published

on

‘Yan bindigar dai sun aukawa jami’ar kimiyya da fasaha ne dake garin Osara a ƙaramar hukumar Adabi a jihar Kogi inda bayan jikkata wasu ɗaliban, sannan suka yi garkuwa da wasu kimanin 57.

Malam Ɗan Asabe wani mazaunin jihar Kogi yace ‘yan bindigar sun haura cikin jami’ar ne ta baya suka dinga harbin kan mai uwa da wabi kamar yadda ya yiwa wakilin Muryar Amurka bayani ta wayar salula.

Tuni dai Gwamnatin jihar Kogin ta yi Allah wadai da wannan hari tare da nuna takaicinta akan lamarin.

Kwamishinan Labarai na jihar Kogin, Kensly Fanwo, yace, kawo yanzu ba su tantance adadin ɗaliban da ‘yan bindigar suka sace ba, amma sun haɗa hannu da jami’an tsaro domin ganin an kuɓuta da ɗaliban cikin ƙoshin lafiya.

KU KUMA KARANTA:’Yan bindiga sun sace ɗalibai a Jami’ar Jihar Kogi

Ya ƙara da cewa, a lokacin da gwamnatin jihar ta samu labarin ta yi ƙoƙarin jibga jami’an tsaro a wannan yanki domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A wata sanarwa daga kakakin ‘yan sandan jihar Kogin, Wilyans Aya, ya ce kwamishinan ‘yan sandan ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin samun nasarar kuɓutar da ɗaliban.

Garkuwa da ɗaliban makaranta dai na ci gaba da ɗaukar hankali a Nijeriya, al’amarin da masana suka ce babbar barazana ce a ɓangaren Ilimi a ƙasar.

Continue Reading

'Yan bindiga

An sace limaman coci 6 a Anambara

Published

on

Rahotanni daga Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu limaman Coci shida yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa birnin Awka na jihar Anambara a kudu maso gabashin Najeriya.

Bayanai sun yi nuni da cewa ‘yan bindigar sun sace Archbishop Uka Uka na Mujami’ar Brotherhood of the Cross and Star, (BCS) da matarsa Anne Osim da ɗansu Ronald Uka Osim.

Sauran limaman Cocin sun haɗa da Azuka Ochu, Moses Okafor da Anderson Akwazie a cewar jaridar Daily Trust.

Jaridar Daily Post ta yanar gizo ta ruwaito cewa mutanen na hanyarsu ta zuwa Awka ne daga jihar Abiya don gudanar da ayyukan wa’azi a lokacin da lamarin ya faru.

Al’amarin ya faru ne a ranar 1 ga watan nan na Mayu kamar yadda rahotanni suka nuna.

KU KUMA KARANTA:An halaka direba da sace mutum 2 a hanyar Abuja

“Mun damu matuƙa, amma muna da tabbacin cewa Ubangijin da suke bautawa zai taimaka musu.” Jaridar ta Daily Post ta ruwaito wani Limami a Cocin ta BCS, Bishop Denis Onuoha yana cewa.

Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar Anambara, ta ce ba ta da masaniyar aukuwar wannan al’amari.

“Ba mu da wasu bayanai da suka nuna aukuwar wannan al’amari a jihar Anambara.” Wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Facebook ta ce a ranar Asabar ɗauke da sa hannun Kakakinta SP Tochukwu Ikenga.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “muna ƙira ga jama’a da su taimaka mana da bayanai kan wannan al’amari idan har ya faru, hakan zai ba mu dama mu ƙaddamar da bincike.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like