No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani ɗan sanda mai suna Judas Chiloane, ya rasa ransa a lokacin da ya je tsaka da yin jima’i da masoyiyarsa a wani daji a yankin Mpumalanga na ƙasar Afirka ta Kudu.

A cewar kafar sadarwa ta Harare a ranar Alhamis, wasu ‘yan bindiga daɗi sun harbe ɗan sandan har sau biyu a kujerar baya ta motarsa ƙirar Ford Ranger bakkie yayin da masoyiyar sa bats samu rauni ƙo kaɗan daga harbin ba.

Rundunar ‘yan sandan Afrika ta Kudu ta kama Charles Mbungeni Mabuza da Howard Mashego a ranar Litinin da ta gabata kan laifin kisan ɗan sandan.

KU KUMA KARANTA: Likitan da yayi wa ƙanwar matarsa ‘yar shekara 15 fyaɗe ya ce ba budurwa ba ce inji shaidu

Kakakin rundunar ‘yan sanda na musamman, Captain Dineo Sekgotodi, ya ce mutanen biyun sun ce sun je wurin ne domin yiwa masoyan fashi, da ke yawan zuwa wurin domin yin lalata a cikin mota, yana mai cewa, “Mutane biyun sun shaida mana cewa za su je wurin da ke kusa da titin Graskop, inda aka harbe Chiloane don yiwa masoyan fashi, waɗanda da ke amfani da yankin don yin jima’i a cikin motarsu.

A cewar Sekgotodi, ‘yan fashin guda biyu da ake zargin sun yi wa Chiloane kwanton ɓauna ne inda suka ƙwace bindigarsa, suka kuma harbe shi a cinyarsa. Lokacin da matar ta bukaci a taimaka, ‘yan sanda sun isa inda aka kashe abokin aikinsu, don kai masa ɗuaki.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...