Yadda Satar notunan titin Jirgin ƙasa ya kawo tangarɗa a sufuri (Bidiyo)

An gano wani lamari mai ban mamaki na satar notuna a hanyar jirgin ƙasa na Abuja zuwa Kaduna, lamarin da ya haifar da matsalar tsaro da kuma yin barazana ga sufurin jiragen ƙasa. Wannan lamari ya bayyana ne a faifan bidiyon da aka ɗauka akan hanyar jirgin.

Satar dai, wadda haryanzu ba a san ko su waye suka aikata ba, ta tayar da hankalin hukumomi da matafiya. Satar ta fito fili lokacin da ma’aikatan jirgin ƙasa da ke gudanar da bincike na yau da kullum suka lura da rashin notuna dayawa akan titin.

Ku KALLI BIDIYON ANAN:

Binciken da aka yi wanda ya tabbatar da satar, ya sa hukumomi cikin ruɗani, fasinjojin kuma sun shiga damuwa game da tsaron lafiyarsu.

Titin jirgin ƙasan daga Abuja zuwa Kaduna na da matuƙar muhimmanci ga harkokin sufurin Najeriya, wanda ya haɗa Abuja babban birnin tarayya zuwa Cibiyar tattalin arziƙin Arewa, Kaduna. Ya kasance hanyar rayuwa ga matafiya da yawa, tana ba da ingantaccen yanayin sufuri mai aminci da inganci tun lokacin da aka ƙaddamar da shi.

KU KUMA KARANTA: Jirgin ƙasa ya tsallake rijiya da baya a hanyar Abuja zuwa Kaduna (Bidiyo)

Wannan lamarin ya haifar da babban haɗari ga lafiyar dubban matafiya na yau da kullum. Notunan da aka sace ba wai kawai suna nuna zalincin masu laifin ba ne kawai, hakan ya nuna rashin imani da halin ko in kula ga lafiyar mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

Ku tuna cewa Neptune Hausa ta ruwaito, a ranar 15 ga wannan watan cewa, fasinjojin jirgin ƙasan sun sauka tare da jigilar kayansu da ƙafa a lokacin da wani jirgin ƙasa da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna, wanda ba zato ba tsammani ya kufce daga kan titinsa, ya bi ta wata hanya daban.

A cikin wani faifayin bidiyo da aka ɗauka, wani fasinja ya yi sharhi da cewa lamarin zai iya yin muni da ace jirgin yana tafiya da sauri. Wani fasinja ma, a cikin bidiyon ya nuna mamaki ganin cewa rashin notuna ne ya janyo jirgin ya rasa hanyar.

Wannan yanayi mai hatsari ya haifar da barazana a lafiyar fasinjoji, ma’aikatan jirgin ƙasa, da ma al’ummomin da ke kusa.

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC) ta yi gaggawar ɗaukan mataki kan lamarin, inda ta haɗa gwiwa da hukumomin tsaro domin gudanar da bincike kan satar tare da cafke waɗanda ke da hannu a lamarin.

An ƙarfafa matakan tsaro a kan hanyar, tare da ƙara yawan sintiri da sanya ido da nufin hana duk wani zagon ƙasa ko ƙeta.

Don rage tashe-tashen hankula da tabbatar da amincin fasinja, NRC ta dakatar da ayyukan jirgin ƙasa na ɗan lokaci har sai an shawo kan matsalar.

Ana gudanar da wasu shirye-shiryen sufuri na daban ga fasinjoji har sai an gyara titin da ya lalace kuma an mayar da duka notunan da aka sace.

Satar layin dogo daga Abuja zuwa Kaduna ya janyo cece-ku-ce a tsakanin ‘yan ƙasa kan buƙatar inganta matakan tsaro.

Hukumomin ƙasar sun yi alƙawarin samar da ƙarin kayan aiki don hana aukuwar lamarin da kuma kare muhimman ababen more rayuwa a faɗin kasar.

Dangane da wannan koma-baya, hukumar ta NRC ta jajirce wajen maido da cikakken aiki a hanyar jirgin Abuja zuwa Kaduna cikin gaggawa.

Babban fifikon su ba wai tabbatar da tsaron lafiyar fasinjojin ba ne, har ma da aikewa da saƙo mai ƙarfi cewa ba za a amince da irin wannan aika aika ba.


Comments

2 responses to “Yadda Satar notunan titin Jirgin ƙasa ya kawo tangarɗa a sufuri (Bidiyo)”

  1. […] KU KUMA KARANTA: Yadda Satar notunan titin Jirgin ƙasa ya kawo tangarɗa a sufuri (Bidiyo) […]

  2. […] KU KUMA KARANTA: Yadda Satar notunan titin Jirgin ƙasa ya kawo tangarɗa a sufuri (Bidiyo) […]

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *