No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’in hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ya harbe wani matashi mai suna Auwal Hassan dan shekaru 30 a duniya, a wani gangamin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar APC a ranar lahadi a garin Bojude da ke ƙaramar hukumar Kwami a jihar Gombe.

Wanda aka harba, ya bi sahun sauran mutanen ƙauyen, inda suka fito domin karɓar tawagar yakin neman zaɓen Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

Shaidun gani da ido sun shaida wa jaridar Dailytrust cewa, bindigar jami’an DSS ta bindige Hassan a kafarsa a yayin da ake ta hayaniya bayan da ayarin motocin gwamnan suka isa wurin da ake gudanar da yaƙin neman zaɓen.

KU KUMA KARANTA:Zaben 2023: an buƙaci ‘yan siyasa da gujewa yin amfani da ƙananan yara yayin gangamin siyasa

Rahotanni sun bayyana cewa wanda aka harba ɗin ya faɗi ƙasa, yana jin zafin harbin da aka mishi, lamarin da ya harzuka wasu matasan da suka fara cewa “Ba mayi” (ba ma goyon bayan ku) a wajen taron yakin neman zaɓen.

Sauran jami’an tsaron tawagar gwamnan sun yi kokarin kwantar da hankalin matasan da suka fara hayaniya.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan faruwar lamarin, Gwamna Yahaya na Gombe ya bada umarnin a kamo jami’an DSS domin gudanar da bincike cikin gaggawa.

Ya kuma bayar da umarnin a kai wanda aka harba, zuwa asibiti domin yi masa magani da kuɗin gwamnatin jihar.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa ya naɗa wanda aka harban, tare da wasu matasa huɗu daga garin Bojude a matsayin masu taimaka masa (PA).

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

4 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...