No menu items!

Sample Page Title

Date:

Fitacciyar jarumar fina-finan Nollywood, Chita Agwu, ta bayyana cewa an sace mata kayanta masu daraja a tashar Finchley Road dake birnin Landan.

Wannan dai na zuwa ne ‘yan makwanni bayan da wasu fitattun jaruman suka yi magana game da haɗuwar su da ‘yan fashi da makami a Landan. Hakanan, Gwamnatin Tarayya ta gargadi ‘yan Najeriya game da ƙaruwar yiwuwar yin fashi a Burtaniya da Amurka.

Jarumar ta bayyana hakan ne a shafin ta na Instagram a ranar Alhamis awani sako da ta wallafa inda ta rubuta cewa, “Ya Allah! Me wannan duniyar ta zama? Ta yaya mutum zai yi barci idon sa biyu a rufe cikin dare, ya sani sarai cewa ya yi wa wani sata?

“An yi min sata a Landan, a tashar Finchley Road. Duk kayana masu daraja a cikin jaka sun tafi. “Na ɗauka mafarki nake yi, ba lafiya, na kasa yin barci jiya da daddare.” in ji jarumar.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...