No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani mutum mai shekaru 43 da aka kai wa takardar sammaci ya soka wa ma’aikacin kotun wuka ya kashe shi.

Mutumin ya yi wa akawun kotun wannan aika-aika ne a unguwar Kugama Wuro Jibir, ƙaramar hukumar Mayo Belwa da ke Jihar Adamawa.

Ma’aikacin kotun mai suna Yauba Usman ya kai masa takardar sammaci ne daga kotun yanki na Nasarao Jereng, amma mutumin ya ƙi karɓa.

A maimakon haka, sai mutumin ya zaro wuka ya rika soka wa ma’aikacin kotun, ya ji masa raunuka, lamarin da ya sa aka kai shi asibiti, amma rai ya yi halinsa.

KU KUMA KARANTA: Ɗan sanda ya kashe abokin aikinsa, ya harbe kansa

Kakakin ’yan sandan jihar Adamawa, SP Sulaiman Nguroje ya ce a sakamakon haka rundunarsu ta cafke wanda ya yi wannan aika-aika, ana masa tambayoyi a ofishinsu.

SP Nguroje ya ce kwamishinan ’yan sandan jihar, Afolabi Babata ya ba da umarni a zurfara bincike a kan lamarin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...