No menu items!

Sample Page Title

Date:

Bayan ɗaurin aurensu da wata biyu kacal, wata matar aure mai suna Salamatu Suleiman, ta shigar da ƙara kotu akan a raba auren, saboda rashin lafiyar mijinta.

Mai shigar da ƙarar ta shaida wa kotun cewa ta lura maniyyin mijin na ta ba shi da kauri.

Ta roƙi kotu da ta raba auren, inda ta ce ta gaji da auren.

Wanda ake ƙara ya yarda cewa yana da matsalar lafiya, amma ya dage cewa matar ma tana da ƙalubalen lafiya ita ma.

Sai dai ya ce har yanzu yana son matarsa ​​kuma ya roƙi kotu da ta ba shi lokaci domin ya sasanta rikicin.

KU KUMA KARANTA: Matata ta auri wani mutum a asirce – miji ya shaida wa kotu

Alƙalin kotun mai shari’a Abdulƙadir Umar ya shaida wa uwargidan da ta kasance da hankali da kuma neman agajin lafiya a kan ƙalubalen da suke fuskanta.

Alƙalin ya shawarci matar da ta ba da dama ta biyu a zamantakewar su, inda ya nuna cewa duk aure yana da ƙalubale.

Kotun ta ɗage sauraren ƙarar zuwa ranar 28 ga watan Agusta, domin samun rahoton sasantawa ko kuma ci gaba da sauraron ƙarar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

5 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...