Connect with us

Al'ajabi

Wata mata ta ciji al’aurar sirikin ta

Published

on

Wani dattijo mai shekaru 78 a mazabar Bumula da ke gundumar Bungoma ta Kenya, yana fama da raunuka a al’aurarsa bayan da aka yi zargin surukarsa ta yi masa awata hatsaniya.

A kokarin da ake na sasanta rikicin da ya ɓarke tsakanin matar da kawarta a gidansu da ke ƙaramar hukumar Kimaeti a ranar Asabar, 28 ga watan Janairu, 2023, an ce Evelyn Okello, matar dansa ta biyu ce ta kai wa Vincent Barasa hari.

Da yake magana da Citizen TV Kenya a ranar talata 31 ga Janairu, Barasa ya ce yana cin abinci da misalin karfe 4 na yamma sai ya ji hayaniya a gidan ɗansa Godfrey Wekesa.

KU KUMA KARANTA:Wasu fusatattun mata su 8 sunyiwa matar aure duka a Jihar Kano

Ɗaya daga cikin jikokinsa ya sanar da shi cewa surukarsa na faɗa da wata mace daga wata kasuwa da ke kusa. Nan da nan ya garzaya wurin da lamarin ya faru a kokarinsa na sasanta rikicin amma ya ci karo da shi inda ya yanke shawarar komawa baya ba tare da wani kokari ba.

Bai daɗe da komawa ba, Evelyn ta bi shi ta buge shi da dutse. Ya faɗi a sume, matar ta zauna masa a kirji tana cizon shi. Kokarin da dattijon ya yi na ture ta ya ci tura, sai ta koma ta cije al’aurarsa.

“Lokacin da nake komawa, ga alama matar ta fusata don haka ta jefe ni da dutse ta bugi bayan kaina. Sai ta ci gaba da cizon al’aura ta.” ya bayyana.

Bayan afkuwar lamarin, fusatattun mazauna wurin da suka isa wurin sun yi wa matar da mijinta dukan tsiya kafin su ɗauki dattijon domin yi musu magani.

Wekesa ya ce matarsa ​​tana yawan samun tashin hankali kuma sau da yawa tana zargin cewa za ta kashe shi da ɗiyarsa.

A halin da ake ciki dai, ‘yan sanda na ci gaba da zakulo wanda ake zargin wanda tuni ta ɓuya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Al'ajabi

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Published

on

An ƙona mutane suna Sallar Asuba a masallaci a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano a arewacin Najeriya ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da cinna wa wani masallaci wuta yayin da mutane ke Sallar Asuba ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Gadan da ke Ƙaramar Hukumar Gezawa a jihar ta Kano, da misalin karfe 5:20 lokacin da ake sallah, a cewar sanarwa ‘yan sanda.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa da TRT Afrika Hausa faruwar lamarin da kama mutumin da ake zargi, sai dai ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike.

Abdullahi Kiyawa ya ce bincike ya nuna cewa mutumin da ake zargi da cinna wutar Shafi’u Abubakar mai kimanin shekaru 38 ya jefa wata roba ne ɗauke da fetur cikin masallacin, sannan ya cinna wuta.

KU KUMA KARANTA: Mahara a Anambara sun ƙona fadar babban Basarake ƙurmus

Kakakin ‘yan sandan ya ce mutum 24 ne suka ƙone a masallacin, da suka haɗar da manya 20, yara huɗu.

An garzaya da duka waɗanda suka jikkata zuwa asibiti don ba su kulawa, amma babu wanda ya mutu a haɗarin, a cewar sanarwar ‘yan sandan.

Continue Reading

Al'ajabi

An tsinci gawar wata ɗaliba a cikin ɗaki a Kano

Published

on

An tsinci gawar wata ɗaliba mai suna Aisha Yahaya ta Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, a wani gida da ke wajen jami’ar.

Aisha, ɗaliba ce da ke matakin karatu na uku wato ‘level 300’ a sashen nazarin Kimiyya da Fasahar Abinci na jami’ar wadda aka tsinci gawarta bayan ta koma ɗakinta.

An ce ɗalibar ta rubuta jarrabawarta ta farko a zangon karatun na farko da ake yi a jami’ar.

Wasu daga cikin abokan karatunta sun danganta mutuwarta da shiga cikin matsi da damuwa a dalilin karatu da kuma zana jarrabawar.

A cikin wasiƙar ta’aziyyar, hukumar jami’ar ta bayyana matuƙar baƙin cikinta dangane da rasuwar Aisha Yahaya.

KU KUMA KARANTA: An tsinci gawar wani mutum a kan titi a Kano

Sanarwar ta ce, “Aisha ɗaliba ce mai hazaƙa wadda ta rasu a dalilin bugun zuciya. Za a riƙa tunawa da ita a kan sha’awarta na karatu da jajircewarta kan harkokin karatunta.”

Jami’ar ta ƙara da cewa, ba a iya gano wata da ke tattare da ita ba gabanin mutuwarta saboda ba ta nuna alamun rashin lafiya ko fama da wata cuta ba.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like