No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani ya ƙone budurwa saboda ta ƙi auren shi

An gurfanar da wani mutum mai suna Abdullahi Idris, a gaban kotun shari’ar Musulunci a Jihar Kano, saboda zargin ƙone budurwarsa, Sa’adatu Ibrahim, saboda ta ƙi amincewa da aurensa.

Idris, wanda yake zaune a garin Rimi, ƙaramar hukumar Sumaila, ya kasance yana soyayya da Sa’adatu, wadda bazawara ce.

Ya shafe tsawon kwanaki bakwai yana muradin ta amince da batun aurensa amma ta ƙi amincewa da buƙatar tayin da ya mata.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta cinye ɗaruruwan shaguna a kasuwar Gwarzo

An tuhume shi da laifin yin sharri, ƙone mutum, da yunƙurin kisan kai, sai dai duk da haka ya musanta dukkanin tuhume-tuhumen da ake masa.

Lauyan mai shigar da ƙara, Barrista Maryam Jubril, ta nemi a ɗage shari’ar zuwa wani lokaci.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...