No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Wani soja da ke aiki da Bataliya ta 35 ta Artillery Brigade na sojojin Najeriya a Abekuta, ya harbe kansa har lahira bisa kuskure.

Sojan ya mutu ne sakamakon harbin da ya yi wa kansa bisa kuskure, in ji kakakin runduna ta 81 ta sojojin Najeriya mai kula da bataliyar, Laftanar-Kanar Olabisi Ayeni ya bayyana a ranar Laraba.

Ayeni ya bayyana cewa, da jin ƙarar harbin na bazata, sai abokan aikin marigayin sun garzaya wurin da lamarin ya faru suka same shi a kwance cikin jini kace-kace.

“Tun daga lokacin ne aka fara bincike don gano al’amura da kuma yiwuwar musabbabin faruwar lamarin.

“An ɗauke gawar sojan tare da ajiye ta a cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Abekuta,” in ji Mista Ayeni.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...