No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wani harin haɗin-gwiwa na Amurka da Birtaniya ya kashe mutum biyu a Yemen

Sojojin Amurka da na Birtaniya sun sanar cewa sun kai hare-hare kan mayaƙan Houthi da ke Yemen.

Ranar Alhamis kafar watsa labarai ta Houthi ta tabbatar da kisan aƙalla mutum biyu a hare-haren.

Ma’aikatar tsaron Birtaniya ta ce an kai hare-haren na haɗin-gwiwa ne a wurare uku a birnin Hodeidah da ke gaɓar Bahar Maliya.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Amurka za su kammala ficewa daga Nijar 15 ga Satumba

Gidan talbijin na Al Masirah wanda ƙungiyar Houthi take gudanar da shi ya ruwaito cewa an kashe aƙalla mutum biyu sannan aka jikkata mutum 10 a hare-haren da aka kai a wani gini na gidan rediyo a lardin Al-Hawk na birnin Hodeidah.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...