Ukraine ta kai ƙazamin hari kan yankunan iyaka na Rasha

0
54
Ukraine ta kai ƙazamin hari kan yankunan iyaka na Rasha

Ukraine ta kai ƙazamin hari kan yankunan iyaka na Rasha

Dakarun Ukraine sun kai farmaƙi a yankunan kan iyakar da safiyar Talata, a wani hari da ya kasance mafi girma da samun nasara da Kyiv kai a cikin shekaru 2 da rabi na yaƙin.

Rasha ta fada jiya Asabar cewa ta kwashe dubban mutane daga yankin kan iyakarta, tare da ƙaddamar da farmakin yaƙi da ta’addanci, a daidai lokacin da take ƙoƙarin shawo kan wani babban kutse na Ukraine.

A lokaci daya kuma, Moscow ta yi gargadin cewa fadan da ake gwabzawa a yankin Kursk da ke yammacin kasar Rasha na yin barazana ga wata tashar makamashin nukiliya.

Dakarun Ukraine sun kai farmaki a yankunan kan iyakar da safiyar Talata, a wani hari da ya kasance mafi girma da samun nasara da Kyiv kai a cikin shekaru 2 da rabi na yakin.

Dakarun ta sun dada matsawa gaba da tazarar kilomita da dama, lamarin da ya tilastawa sojojin Rasha yin gaggawar waiwayar wurin ajiyar makamai da karin kayan aiki, ko da yake babu wani bangare da ya ba da cikakken bayani kan adadin sojojin da aka sanya.

KU KUMA KARANTA:Ƙasar Mali ta yanke hulɗa da Ukraine kan zargin goyon bayan ‘yan ta’adda

Jami’an yankin sun yi cikakken bayani kan yadda fararen hula da sika fice daga garuruwa da kauyukan da ke kusa da yankin da ake gwabzawa.

Sama da mutane 76,000 ne aka kwashe su na wucin gadi zuwa wasu wuraren tudun mun tsira,” kamar yadda kamfanin dillancin labarai na gwamnati TASS, ya ruwaito wani jami’in ma’aikatar kula da ayukan gaggawa na yankin yana fada a wani taron manema labarai a jiya Asabar.

An kai agajin gaggawa zuwa yankin kan iyaka, an kuma sanya karin jiragen kasa zuwa babban birnin kasar, Moscow, ga mutanen da suka arce wa yakin.

Amma da yammacin ranar Asabar ɗin, an yi ta harbe-harbe ta sama a Kyiv, babban birnin ƙasar Ukraine.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here