No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tsohuwar ministar ayyuka da jin-ƙai ta Najeriya Sadiya Umar Farouq ta kai kanta a gaban hukumar EFCC a Abuja babban birnin Najeriya.

Ana zargin wani kwangila a ma’aikatarta da almundahanar sama da naira biliyan 37.

Tun a makon da ya gabata ne hukumar ta gayyaci tsohuwar ministar ta gabatar da kanta, sai dai wasu majiyoyi sun tabbatar da ba ta je ba.

A safiyar Litinin tsohuwar ministar ta fitar da sanarwa a shafinta na X inda ta sanar da zuwanta hukumar.

KU KUMA KARANTA: EFCC ta gayyaci tsohuwar ministar Buhari, Sadiya Farouk

“Bisa radin kaina, na isa hedikwatar hukumar da ke yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zango ƙasa (EFCC) domin karɓar goron gayyata domin ƙarin haske dangane da wasu lamura waɗanda hukumar ke bincike a kai,”

Sai dai a kwanakin baya, tsohuwar ministar ta wallafa wani saƙo a ranar 26 ga watan Disambar 2023 inda take nesanta kanta daga duk wasu rahotanni da ke nuna cewa EFCC na bincike a kanta inda hasalima ta yi zargin ana ƙoƙarin ɓata mata suna.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...