Connect with us

Kasashen Waje

Trump yana jinya a asibiti bayan da aka ji masa rauni wajen yaƙin neman zaɓe

Published

on

Trump yana jinya a asibiti bayan da aka ji masa rauni wajen yaƙin neman zaɓe

Trump yana jinya a asibiti bayan da aka ji masa rauni wajen yaƙin neman zaɓe

Ofishin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya fitar da wata sanarwa inda ya bayyana cewa, tsohon Shugaban ƙasar ya samu rauni a fuska a ranar Asabar, amma yana “lafiya” bayan da aka harba bindiga a wajen da ya ke wani gangamin yaƙin neman zaɓe a Pennsylvania.

Ofishin yaƙin neman zaɓen Trump ya ce ana kulawa da ɗan takarar shugaban ƙasar na jam’iyyar Republican a wani asibiti da ke garin Butler.

Trump ya je garin Butler da ke ɗaya daga cikin jihohin da ba su da tsayyen ɗan takara, domin gudanar da wani taro.

Kakakin ofishin yaƙin neman zaɓen Tump Steven Cheung ya faɗa a cikin wata sanarwa cewa, “Shugaba Trump ya godewa jami’an tsaro da jami’an agajin gaggawa saboda ɗaukar mataki nan da nan yayin wannan ɗanyen aikin, yana lafiya kuma ana duba lafiyarsa a wani asibitin gida.”

KU KUMA KARANTA:Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Mutane sun ji ƙara masu kama da harbin ƙananan bindigogi kafin tsohon Shugaban ya kama gefen fuskarsa ya noƙe a bayan dogon teburin da yake tsaye yana magana. Nan da nan jami’an leƙen asiri suka yi wuf suka kakkange shi. Ana jin yana cewa “bari in ɗauko takalmina,” kafin ya miƙe tsaye, jami’an leƙen asiri suna kewaye da shi.

An ga jini yana kwarara daga kunnensa na dama, ya kuma yi ta cewa, akai-akai, ” jira.” Daga nan ya ɗaga hannu na dama ya tsira hannu yana nuna tsakiyar taron ya maimaita kalma guda ɗaya sau uku.

Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leƙen asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Wannan yanzu bincike ne na ma’aikatar tsaron, kuma za a fitar da ƙarin bayani nan gaba.”

Fadar White House ta aikawa manema labarai wata sanarwa cewa, Shugaba Joe Biden “ya sami bayanin farko game da abin da ya faru a taron tsohon Shugaba Trump.” Bayan ‘yan mintoci kaɗan, su ka ce manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da shugaban hukumar leƙen asiri, da manyan hadimai da kuma sakataren tsaron cikin gida su na yi wa Shugaban ƙasar bayani a kan lamarin.

Ofishin Mataimakiyar Shugaban ƙasar kuma ya shaida wa manema labarai cewa, ana yi wa Mataimakiyar Shugaban ƙasar bayanin farko.

Babban Lauyan ƙaramar Hukumar Butler, Richard Goldinger ya shaidawa Kamfanin Dillancin Labarai na Associated Press cewa, dan bindigar da ake zargin ya mutu, kuma an kashe aƙalla mutum guda daga cikin waɗanda su ka halarci taron.

Click to comment

Leave a Reply

Kasashen Waje

Shugaban Bangladash na riƙon ƙwarya ya yi ƙiran da a kai zuciya nesa

Published

on

Shugaban Bangladash na riƙon ƙwarya ya yi ƙiran da a kai zuciya nesa

Shugaban Bangladash na riƙon ƙwarya ya yi ƙiran da a kai zuciya nesa

Yunus mai shekaru 84, da ya taɓa lashe kyautar Nobel, ya dawo daga Turai a wannan makon don jagorantar gwamnatin wucin gadi, da ke fuskantar babban ƙalubale na kawo ƙarshen rikice-rikice da aiwatar da sauye-sauyen dimokuraɗiyya.

A jiya Asabar shugaban riƙon ƙwarya na Bangladesh Muhammad Yunus ya yi ƙira ga samun haɗin kan addinai bayan ganawa da mahaifiyar ɗalibar da ‘yansanda suka harbe har Lahira, lamarin da ya janyo zanga-zangar da ta kawo ƙarshen mulkin Sheikh Hasina na tsawon shekaru 15.

Yunus mai shekaru 84, da ya taba lashe lashe kyautar Nobel, ya dawo daga Turai a wannan makon don jagorantar gwamnatin wucin gadi, da ke fuskantar babban kalubale na kawo karshen rikice-rikice da aiwatar da sauye-sauyen demokradiyya.

Ya shaida wa manema labarai cewa “Hakinmu shi ne gina sabuwar Bangladesh,”

Hare-haren ramuwar gayya da aka kai kan mabiya addinin Hindu tsiraru a kasar tun bayan hambarar da gwamnatin Hasina, ya haifar da fargaba a makwabciyar kasar Indiya da kuma fargaba a cikin gida.

A yayin wata ziyara da ya kai birnin Rangpur da ke arewacin kasar, Yunus ya yi kira da a kwantar da hankali, ta hanyar tunawa da karrama Abu Sayeed, dalibi na farko da aka kashe a rikicin na watan jiya.

KU KUMA KARANTA:Firaministar Bangladesh, Sheikh Hasina, ta sauƙa daga mulki

Ya kara da cewa “Abu Sayeed yanzu yana cikin kowane gida, yadda ya tsaya muma haka muke yi”. “Babu bambance-bambance a Bangladesh ta Abu Sayeed.”

A ranar 16 ga watan Yuli ne ‘yan sanda suka harbe Sayeed, mai shekaru 25, sa’adda ‘yan sanda suka fara kai farmaki kan masu zanga-zangar da dalibai suka jagoranta ta kin jinin gwamnatin Hasina.

Hasina, mai shekaru 76, ta fice daga kasar da jirgin sama mai saukar mai saukar ungulu zuwa makwabciyar kasar Indiya a ranar Litinin, yayin da masu zanga-zangar suka mamaye titunan Dhaka a wani gagarumin yunkurin kai karshen mulkinta.

Ana zargin gwamnatinta da cin zarafin bil adama da suka hada da kisan gillar da aka yi wa dubban abokan hamayyarta na siyasa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Ukraine ta kai ƙazamin hari kan yankunan iyaka na Rasha

Published

on

Ukraine ta kai ƙazamin hari kan yankunan iyaka na Rasha

Ukraine ta kai ƙazamin hari kan yankunan iyaka na Rasha

Dakarun Ukraine sun kai farmaƙi a yankunan kan iyakar da safiyar Talata, a wani hari da ya kasance mafi girma da samun nasara da Kyiv kai a cikin shekaru 2 da rabi na yaƙin.

Rasha ta fada jiya Asabar cewa ta kwashe dubban mutane daga yankin kan iyakarta, tare da ƙaddamar da farmakin yaƙi da ta’addanci, a daidai lokacin da take ƙoƙarin shawo kan wani babban kutse na Ukraine.

A lokaci daya kuma, Moscow ta yi gargadin cewa fadan da ake gwabzawa a yankin Kursk da ke yammacin kasar Rasha na yin barazana ga wata tashar makamashin nukiliya.

Dakarun Ukraine sun kai farmaki a yankunan kan iyakar da safiyar Talata, a wani hari da ya kasance mafi girma da samun nasara da Kyiv kai a cikin shekaru 2 da rabi na yakin.

Dakarun ta sun dada matsawa gaba da tazarar kilomita da dama, lamarin da ya tilastawa sojojin Rasha yin gaggawar waiwayar wurin ajiyar makamai da karin kayan aiki, ko da yake babu wani bangare da ya ba da cikakken bayani kan adadin sojojin da aka sanya.

KU KUMA KARANTA:Ƙasar Mali ta yanke hulɗa da Ukraine kan zargin goyon bayan ‘yan ta’adda

Jami’an yankin sun yi cikakken bayani kan yadda fararen hula da sika fice daga garuruwa da kauyukan da ke kusa da yankin da ake gwabzawa.

Sama da mutane 76,000 ne aka kwashe su na wucin gadi zuwa wasu wuraren tudun mun tsira,” kamar yadda kamfanin dillancin labarai na gwamnati TASS, ya ruwaito wani jami’in ma’aikatar kula da ayukan gaggawa na yankin yana fada a wani taron manema labarai a jiya Asabar.

An kai agajin gaggawa zuwa yankin kan iyaka, an kuma sanya karin jiragen kasa zuwa babban birnin kasar, Moscow, ga mutanen da suka arce wa yakin.

Amma da yammacin ranar Asabar ɗin, an yi ta harbe-harbe ta sama a Kyiv, babban birnin ƙasar Ukraine.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mutane 9 ne suka mutu a rikicin ‘yan bindiga a Libya

Published

on

Mutane 9 ne suka mutu a rikicin ‘yan bindiga a Libya

Rikicin ya samo asali ne daga yunƙurin kashe Al-Baqra da aka yi a ranar Juma’a, wanda mayaƙansa suka ɗaura alhakinsa kan al-Shahida Sabriya, kamar yadda kafafen yaɗa labaran ƙasar suka rawaito.

Jami’ai a kasar Libiya sun ce fadan da aka gwabza tsakanin wasu kungiyoyin ‘yan bindiga masu dauke da manyan makamai a babban birnin kasar ya firgita mazauna yankin tare da kashe mutane kusan dozin daya, tashin hankali na baya bayan nan a wannan kasa ta arewacin Afirka da mafi yawanta babu doka da oda.

Jami’an sun kara da cewa, fadan da aka shafe sa’o’i ana gwabzawa, wanda ya hada da manyan makamai, ya faru ne a ranar Juma’a a unguwar Tajoura da ke gabashin birnin Tripoli ko Turabulus, tsakanin mayakan Rahba al-Duruae, karkashin jagorancin jagoran yaki Bashir Khalfallah, wanda aka fi sani da al-Baqrah, da kuma wata kungiyar ‘yan bindiga ta al-Shahida Sabriya.

Sashen Motocin Daukar Marasa Lafiya da Ayyukan Gaggawa na Ma’aikatar Lafiyar kasar ya ce akalla mutane 9 ne suka mutu, sannan wasu 16 suka jikkata a rikicin da aka kwashe sa’o’i ana yi.

Rikicin ya samo asali ne daga yunkurin kashe al-Baqra da aka yi a ranar Juma’a, wanda mayakansa suka daura alhakinssa kan al-Shahida Sabriya, kamar yadda kafafen yada labaran kasar suka rawaito.

Khaled al-Meshry, wanda shi ne sabon shugaban majalisar gudanarwar kasar da ke yammacin kasar, ya yi Allah wadai da yunkurin kisan gillar da aka yi, tare da yin kira da a gudanar da bincike domin hukunta wadanda suka aikata laifin.

KU KUMA KARANTA:Libya ta kora ‘yan Najeriya da Mali 463 Zuwa Nijar

Bangarorin biyu da ke gaba da juna suna kawance da gwamnati Firai minista Abdul Hamid Dbeibah.

Sai dai kakinta bai amsa bukatar yin magana kan lamarin ba.

Tashin hankalin dai ya nuna raunin kasar Libiya bayan boren da aka yi a shekarar 2011, da ya rikide ya koma yakin basasa, wanda ya kifar da gwamnatin Moammar Gadhafi da ya dade yana mulki kama karya.

Yayin da ake cikin rikicin, mayaƙan sun samu ƙaruwar dukiya da iko, musamman a Tripoli da yammacin ƙasar.

Continue Reading

You May Like