No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na shirin naɗa Olanipekun Olukoyede a matsayin babban shugaban hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa ta EFCC.

Alfijir Labarai ta rawaito Lauyan mai suna Olukoyede ya yi aiki a matsayin sakataren EFCC na tsawon shekaru biyu a ƙarƙashin tsohon shugaban riƙo Ibrahim Magu.

An dakatar da shi daga aiki tare da Magu a shekarar 2020 kuma ba a sake ƙiransa ba.

Kafin aikinsa na sakatare, Olukoyede shi ne shugaban ma’aikatan Magu.

Ana sa ran za a sanar da naɗin nasa, wanda ke buƙatar amincewar Majalisar Dattawa “nan ba da jimawa ba,” a cewar majiyoyin da ke da masaniya kan ci gaban.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...