No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin dawo da shirin Gwamnatin Tarayya na ciyar da ɗalibai a makarantu.

Tinubu ya dawo da shirin ciyar da ɗaliban ne da nufin rage yawan ƙananan yara marasa zuwa makaranta da suka gararamba a kan tituna.

Gwamnatin da ta gabace shi, ta tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ce ta dakatar da tsarin bayan shekaru da farawa.

Amma Tinubu ya ce dawo da tsarin zarin samar da mafita daga matsalar rashin zuwa makaranta a tsakanin yaran.

A cewarsa, muddin ba a magance matsalar da yaran suke fuskanta a wajen neman ilimi ba, magance matsalar rashin zuwa makarantar yara zai yi wuya.

KU KUMA KARANTA: Gwamna Buni ya nemi haɗin kan jami’o’in Burtaniya uku, don bunƙasa harkar ilimi a jihar Yobe

Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman, ne ya sanar da hakan a taron laluɓo hanyoyin samun nasara da a ma’aikatar ilimi daga 2023 zuwa 2027.

Ministan ya ce shugaban ƙasa ya ɗauke ciyarwan daga hannun ma’aikatar ayyukan agaji ya dawo da shi ƙarƙashin Ma’ikatar Ilimi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...