Connect with us

Kasashen Waje

Taron ƙungiyar AU na nemo hanyar warware matsalolin da ke addabar nahiyar Afirka

Published

on

Shugabannin ƙasashen Afirka sun buɗe wani taro na kwanaki biyu a ranar Asabar, yayin da nahiyar ke kokawa da juyin mulki da rigingimu da rikicin siyasa da kuma zaman ɗar-ɗar a yankin.

Gabanin taron da za a yi a Addis Ababa babban birnin ƙasar Habasha, shugaban hukumar Tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat, ya yi tsokaci kan tashe-tashen hankula da ke addabar kasashe da dama, na Afirka da sauran sassan duniya.

Sudan na cikin “rikici,” in ji Faki, yayin da yake bayyana barazanar ‘yan ta’adda a Somaliya, da “rikicin marar ƙarewa” a gabashin Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo, da “haɗarin ta’addanci” a yankin Sahel, da kuma rashin zaman lafiya a Libya.

“Sake dawo da juyin mulkin soji da tashin hankali kafin zaɓe da bayan zaɓe, da rikicin jin ƙai da ke da nasaba da yaƙi da ko kuma illar sauyin yanayi, duk wani abu ne mai matuƙar damuwa a gare mu,” kamar yadda ya shaida wa ministocin harkokin wajen Afirka a ranar Laraba.

An buɗe ƙaramin taron ƙolin da nufin lalubo hanyoyin sake ƙaddamar da shirin samar da zaman lafiya ga DR Congo ciki har da shugaban Congo da abokin hamayyarsa na Ruwanda, wanda aka buɗe ranar Juma’a a gefen manyan tarukan ƙungiyar AU, kuma zai ci gaba a ranar Asabar.

Sai dai an daɗe ana sukar ƙungiyar mai mambobi 55 da cewa ba ta da wani tasiri, kuma ba ta ɗauki ƙwararan matakai ba wajen fuskantar tashe-tashen hankula da ƙwace madafun iko.

KU KUMA KARANTA:Turkiyya na fatan bunƙasa kasuwanci da Saudiyya zuwa dala biliyan 30

Nina Wilen, daraktan shirin Afirka a cibiyar nazarin hulɗar ƙasa da ƙasa ta Egmont Royal da ke Brussels, ta ce “Ina shakkun cewa za a yanke hukunci mai ƙarfi.”

Ya zuwa yanzu dai ƙungiyar ta ƙasashen Afirka ba ta da wani tasiri sosai kan ƙasashen da suka fuskanci juyin mulkin baya-bayan nan, in ji ta, ta kuma ƙara da cewa ƙasashe mambobin ƙungiyar ba sa son kafa abubuwan da za su ci karo da muradunsu.

Daga cikin waɗanda suka halarta daga wajen yankin har da shugaban ƙasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva. Sai dai babban sakataren MDD Antonio Guterres bai halarci taron ba, yayin da mai magana da yawunsa Stephanie Tremblay ta shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP, cewa yana da matsalar jirgin sama kuma bai samu damar tashi zuwa Addis Ababa ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Published

on

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta yi Allah wadai da kalaman nuna wariyar launin fata ga ‘yan wasanta a ranar Alhamis, bayan da Panama ta yi nasara a kan Amurka da ci 2-1 a gasar cin kofin Copa America.

A wani saƙo da ta wallafa a shafin X, hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta ce “Babu shakka, babu wuri a cikin wasa na irin wannan halayya ta nuna ƙiyayya da wariya.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “Waɗannan ayyukan ba kawai ba za’a amince da su ba ne, amma kuma sun saɓa wa kimar mutuntawa da haɗa kai da muka ɗauka a matsayin hukuma.”

KU KUMA KARANTA:Manchester City ta lashe Firimiyar Ingila sau huɗu a jere

Timothy Weah, wanda baƙar fata ne, yana ɗaya daga cikin ‘yan wasan da aka ci zarafin su. An bai wa ɗan wasan gaba na Amurka jan kati kai tsaye a minti na 18 da fara wasa, saboda hannu da ya sa ya bugi ɗan wasan Panama a bayan kan sa a lokacin da ƙwallon ta fita wajen filin wasa.

Ɗan wasan Amurka Folarin Balogun ya zura ƙwallo a minti na 22 da fara wasan bayan an bai wa Weah jan kati kafin ɗan wasan Panama Blackman ya farke a minti na 26.

Fajardo ya zura ƙwallo da ta bai wa Panama nasara da ci 2-1 a minti na 83.

Weah ya fitar da wata sanarwa ta kafafan sada zumunta, inda ya bayar da haƙuri tare da neman gafarar waɗanda ya ɓata wa rai.

Yanzu haka dai Amurka, wacce ita ce ke karɓar baƙuncin gasar cin kofin na Copa America, muddin tana son zuwa zagaye na gaba to dole ne ta yi nasara a wasanta da Uruguay da zura ƙwallaye wanda ko da Panama ta yi nasara kan Bolivia za ta samu tsallake wa.

Continue Reading

Kasashen Waje

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

Published

on

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

An tafka muhawarar farko tsakanin shugaba Biden da Trump

Shugaban Amurka Joe Biden da tsohon shugaban ƙasar Donald Trump sun gwabza muhawara a daren Alhamis, inda suka fafata kan tattalin arziƙin Amurka da harkokin ƙasashen waje da haƙƙin zubar da ciki da kuma batun ƙaura daga kan iyakar Mexico zuwa Amurka.

“Muna tamkar a wata matalauciyar ƙasa a duniya kuma abin kunya ne,” in ji Trump ya faɗa yayin muhawarar da aka watsa ta talabijin ga ƙasa baki ɗaya, daga hedkwatar gidan talabijin na CNN da ke Atlanta.

“Ba a mutunta mu,” in ji Trump, yana zargin Biden. “Suna tunanin mu wawaye ne.”

Biden ya mayar da martani lokaci guda, yana kallon Trump. Tare da cewa “Wannan shi ne shugaban ƙasa mafi muni a tarihin Amurka. Wannan mutumin bai san ma’anar dimokuraɗiyyar Amurka ba.”

Haɗuwar Biden-Trump, watanni huɗu gabanin zaɓen ranar 5 ga watan Nuwamba, ita ce muhawara ta farko da aka taɓa yi a zagaye na huɗu na zaɓen shugaban ƙasar Amurka.

Hakanan sake haɗuwa ne tun muhawarar su guda biyu a shekarar 2020, wanda ya faru a cikin watanni biyu kafin Biden ya kayar da yunƙurin sake zaben Trump na wa’adi na biyu a Fadar White House.

Muhawarar ta ranar Alhamis ita ce karo na farko da shugabannin Amurka biyu suka taɓa yin muhawara a tsakaninsu, kuma shi ne karo na farko, da Biden da Trump suka haɗu a ɗaki ɗaya tun bayan muhawarar da suka yi a watan Oktoban 2020.

KU KUMA KARANTA:Biden ya yi alƙawarin kare Isra’ila daga harin ramuwar gayya na Iran

Trump ya tsallake bikin rantsar da Biden a watan Janairun 2021, kuma tun daga lokacin suka yi ta zage-zage da juna, ciki har da matakin muhawara a daren Alhamis.

A cikin ‘yan kwanakin nan, Trump ya yi ba a game da shirye-shiryen muhawarar Biden, inda ya ba da shawarar cewa zai bukaci ƙarin ƙarfi daga likita don samun damar iya muhawarar ta mintuna 90, gaba da gaba.

Trump ya faɗa wa wani gangamin magoya baya a Philadelphia cewa, “A yanzu haka, Joe ya tafi gidan katako don yin nazari,” yayin da yake zayyana alamomi da hannunsa. “Yanzu yana barci, saboda suna son ya samu ƙarfi.”

Continue Reading

Kasashen Waje

Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

Published

on

Kotun duniya ta umurci Isra’ila ta dakatar da kai farmaki a Rafah

A ranar Juma’a ne babban kotun duniya ICJ ta umarci Isra’ila da ta dakatar da hare-haren da take yi a Rafah, birnin da ke kudancin Gaza inda Falasɗinawa sama da miliyan ɗaya suka nemi mafaka a cikin mawuyacin hali.

Ko da yake da wuya Isra’ila ta bi wannan umarni, wanda babbar kotun Majalisar Ɗinkin Duniya ba ta da hurumin aiwatar da shi, amma hukuncin da aka yanke zai ƙara matsin lamba kan ƙasar.

A ci gaba da ƙalubalantar ɓacin ran da ƙasashen duniya suka yi kan rikicin jin kai a yankin, sojojin Isra’ila sun ci gaba da kai munanan hare-haren da suka ƙaddamar sakamakon hare-haren Hamas na ranar 7 ga watan Oktoba.

KU KUMA KARANTA:Babbar Kotun MƊD ta fara sauraron ƙara kan afka wa Rafah da Isra’ila ta yi

Tattaunawar tsagaita buɗe wuta ta ci tura, duk da matsin lamba da ake yi a gida na firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu na ganin an sako mutanen da a ka yi garkuwa da su a Gaza.

Umurnin na ICJ ya biyo bayan roƙon gaggawa da ƙasar Afirka ta Kudu ta gabatar a wani ɓangare na shari’ar da take ci gaba da yi a kotun da ke birnin Hague na ƙasar Netherlands, inda ta zargi Isra’ila da aikata kisan kiyashi a hare-haren da ta shafe watanni ana kai wa Gaza, zargin da Isra’ila da Amurka suka musanta.

Mai yiyuwa ne shari’ar za ta ɗauki shekaru ana warwarewa, amma Afirka ta Kudu ta nemi umarnin wucin gadi don kare Falasɗinawa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like