Tag: NYSC
-
An ceto sauran ɗaliban Jami’ar Gusau da ’yan NYSC da ke hannun masu garkuwa
’Yan bindiga sun sako ragowar ɗalibai da ma’aikatan Jami’ar Tarayya da ke Gusau, Jihar Zamfara, waɗanda aka yi garkuwa da su a watanni bakwai da suka gabata. A ranar 22 ga Satumbar 2023 ne mahara suka kutsa dakunan kwanan daliban da ke unguwar Sabon-Gida a Karamar Hukumar Bungudu a jihar Zamfara, suka sace dalibai sama da…
-
Hukumar NYSC ta haɗa kai da jami’an tsaro domin ƙubutar da ‘yan hidimar ƙasa da aka sace a Zamfara
Hukumar NYSC ta ce tana aiki tare da jami’an tsaro domin ganin an sako wasu ‘yan masu yi wa ƙasa hidima guda takwas, waɗanda aka yi garkuwa da su a Zamfara a kan hanyarsu ta zuwa sansanin horon da su da ke Sakkwato. Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai da…
-
‘Yan Bindiga a Zamfara, sun buƙaci miliyan huɗu ga ‘yar NYSC da suka sace
Wasu ’yan bindiga sun buƙaci a biya Naira miliyan huɗu a matsayin kuɗin fansa domin sako ɗaya daga cikin masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) da aka sace a jihar Zamfara kwanakin baya. Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun yi garkuwa da wasu mutane 8 da ke kan hanyarsu ta zuwa sansanin masu yi wa…
-
Hukumar NYSC ta tabbatar da yin garkuwa da ɗalibai takwas a Zamfara
Hukumar yi wa ƙasa hidima ta ƙasa (NYSC), ta tabbatar da sace wasu ɗalibai takwas da suka kammala karatu zuwa jihar Sakkwato domin gudanar da zangon rukunin B (Batch B, stream 11 orientation camp). Daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na NYSC, Eddy Megwa, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce wasu ‘yan…
-
Gwamnan Zamfara ya ba da umarnin a gyara sansanin NYSC na jihar
Gwamna Dauda Lawal na Zamfara ya amince da gyara sansanin ‘Permanent Orientation Camp’ na hukumar yi wa ƙasa hidima ta NYSC na dindindin da ke garin Tsafe a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar. Kwamishinan matasa da ci gaban wasanni na jihar, Tasi’u Musa ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a sansanin horar da shirin…
-
Bayan shekara 12 da rufe sansanin NYSC a Borno, an sake buɗe shi
Hukumar Kula da Matasa Masu yi wa Ƙasa Hidima (NYSC) ta fara ba da horo ga matasa masu yi wa ƙasa hidima su 1,161 a sansanin horar da malamai na ATC da ke Jihar Borno. Kimanin shekaru 12 ke nan sansanin ya shafe a rufe sakamakon ta’addancin Boko Haram. Fara horarwar wanda aka shirya yi a ranar Juma’a mai zuwa a Maiduguri, zai…
-
Membobin NYSC 5 za su maimaita shekarar yiwa ƙasa hidima a Bauchi
Rifkatu Yakubu, shugabar hukumar yi wa ƙasa hidima ta ƙasa NYSC reshen jihar Bauchi, ta bayyana cewa biyar daga masu yi wa ƙasa hidima na rukunin ‘Batch B stream 1’ na shekarar 2022, za su maimaita shekarar hidimar su a jihar. Ta bayyana hakan ne ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a Bauchi a…
-
‘Yan sanda sun kama wani ɗan NYSC da ake zargi da aikata fyaɗe a Ogun
Rundunar ‘yan sandan jihar Ogun ta ce ta kama wani memba mai yi wa ƙasa hidima, (NYSC), Adebola Sodiq, bisa zargin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 20 fyade. (an sakaye sunanta). Abimbola Oyeyemi, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abeokuta ranar Asabar. Mista Oyeyemi…
-
Buhari ya taya NYSC murnar cika shekaru 50, ya yabawa Gowon kan hangen nesa
Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya jinjina wa tsohon shugaban ƙasa, Janar Yakubu Gowon mai ritaya, bisa hikimar kafa hukumar yi wa ƙasa hidima ta ƙasa (NYSC), a shekarar 1973. A wata sanarwa da mai magana da yawunsa Femi Adesina ya fitar ranar Juma’a a Abuja, Buhari ya ce da gaske shirin ya cimma burin dunƙulewar…
-
NYSC ta yi tattakin bikin cika shekaru 50 da kafuwa a Yobe
A ci gaba da gudanar da bukukuwan cika shekaru 50 da kafa hukumar yi wa ƙasa hidima ta ƙasa (NYSC) da ta fara gudanar da tattaki na haɗin kai a faɗin ƙasar baki ɗaya domin fara jerin abubuwan da za su ɗauki tsawon mako guda. A jihar Yobe, shugabar NYSC ta jihar (co’ordinator), Hajiya Hafsat…