No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ɓarayi sun sace fitilun titin ɗaya daga cikin filayen jiragen saman Najeriya watanni bayan an saka su.

Mahukunta a filin tashin jiragen saman ne suka tabbatar wa da BBC aukuwar wannan lamari.

Tuni aka ƙaddamar da bincike don kama waɗanda suka aikata wannan sata da kuma dawo da abin da suka sata.

Ba dai a san lokacin da aka sace fitilun a filin tashin jiragen sama na Murtala Muhammed da ke Legas ba.

Kodayake wasu kafafan yaɗa labaran jihar sun ce ana zargin ma’aikatan filin jirgin saman da hannu a wannan sata.

KU KUMA KARANTA: Wasu ‘yan bindiga sun kashe ma’aikacin INEC, sun sace matarsa a Ebonyi

A watan Nuwambar 2022 ne, aka sanya fitilun domin ƙara haske a filin.

Saboda duhun wajen dole aka mayar da jiragen da ke zirga-zirga a tsakanin jihohin Najeriya sauƙa da tashi a ɓangaren tashin jiragen ƙasashen waje.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...