No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin sabuwar hukumar gudanarwa da hukumar alhazai ta ƙasa (NAHCON) ya kuma miƙawa majalisar dattawan Najeriya domin tabbatar da hakan.

Shugaban a cikin ƙudurinsa na tabbatar da gudanar da aikin Hajji na shekarar 2024 ba tare da matsala ba, ya naɗa waɗannan mutane a Hukumar NAHCON:

Jalal Arabi – a matsayin Shugaba

Aliu Abdulrazaq – Kwamishina, Siyasa, Ma’aikata, & Kuɗi

Prince Anofi Elegushi – Kwamishinan Ayyuka

Farfesa Abubakar A. Yagawal – Kwamishinan Tsare-tsare da Bincike

KU KUMA KARANTA: NAHCON ta ba maniyyata aikin hajjin baɗi mako uku su fara biyan kuɗaɗensu

WAKILAN ZONAL:

Dr. Muhammad Umaru Ndagi — Arewa ta tsakiya

Abba Jato Kala — Arewa maso Gabas

Sheikh Muhammad Bin Othman — Arewa maso Yamma

Tajudeen Oladejo Abefe – Kudu maso Yamma

Aishat Obi Ahmed — Kudu maso Gabas

Zainab Musa – Kudu maso Kudu

Professor Musa Inuwa Fodio — Jama’atul Nasril Islam

Farfesa Adedimizi Mahfouz Adebola — Majalisar Koli kan Harkokin Addinin Musulunci

Shugaban ya umurci waɗanda aka naɗa su sadaukar da kansu wajen ganin cewa ayyukan hukumar alhazai ta ƙasa, kuma su kasance masu inganci da gaskiya da kuma biyan bukatun ‘yan Najeriya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...