No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban hukumar zaɓe ta jihar Yobe, Dakta Mamman Mohammed ya rasu

Shugaban hukumar zaɓe ta jihar Yobe (YOSIEC), Dakta Mamman Mohammed (Shamakin Fika) ya rasu.

Ɗansa, Barista Abba Mamman ne ya tabbatar da rasuwarsa.

Dakta Mamman ya rasu ne a asibitin koyarwa na jami’ar jihar Yobe da ke Damaturu, bayan ya yi fama da doguwar jinya.

KU KUMA KARANTA: Marigayi Alhaji Aminu Dantata ya bar mana wasiyar a binne shi a Madina idan ya rasu – Inji iyalansa

Kafin rasuwarsa shi ne shugaban hukumar zaɓe ta jihar Yobe (YOSIEC), sannan shi kwararren likita ne (Medical Doctor), sannan kuma ya riƙe kwamishinan lafiya na jihar Yobe a lokacin mulkin Bukar Abba Ibrahim.

Dakta Mamman ya rasu yana da shekaru 74, ya bar mata 3 da ‘ya’ya 33 rayayyu.

Za a yi jana’izarsa gobe Talata da misalin ƙarfe 1:30 na rana a fadar mai martaba Sarkin Fika da ke Potiskum.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...