No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da shugaban Hukumar Yaƙi da Rashawa da yi wa Tattalin Ariƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), AbdulRasheed Bawa.

Wata sanarwa da ta fito daga ofishin sakataren gwamnatin Tarayya ta ce shugaban ya ɗauki wannan mataki ne domin bayar da damar gudanar da bincike kan wasu manya-manyan zarge-zargen da ke kan Bawa.

Sanarwar, wadda ta samu sa hannun daraktan yaɗa labaru na ofishin sakataren gwamnatin Tarayya, ta ce an bai wa AbdulRasheed Bawa umurnin miƙa aiki ga daraktan gudanarwa na hukumar, wanda zai kula da yadda za a gudanar da binciken.

KU KUMA KARANTA: Hukumar EFCC ta kama mutane 33 da ake zargi da damfara ta yanar gizo

A shekarar 2021 ne dai tsohon shugaban Najeriya, Muhammdu Buhari ya naɗa Bawa, a matsayin shugaban hukumar ta EFCC.

AbdulRasheed Bawa shi ne jami’i mai girman muƙami da sabon shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya dakatar daga aiki bayan kama mulki a ranar 29 ga watan Mayu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...