No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sayyid Khamene’i ya sake naɗa manyan Malamai 3 a majalisar tsaron Iran

A ranar Talata, Jagoran Juyin Juya Hali na Iran, Ayatollah Sayyid Ali Khamenei, ya sake naɗa Ayatollah Alireza Arafi, Ahmad Khatami, da Ahmad Hosseini-Khorasani a matsayin membobin limamai (faqihai) na Majalisar Tsaro (Guardian Council).

Wannan majalisa mai mambobi 12 na da muhimmiyar rawa a tsarin mulkin Iran, tana tantance dokoki, tace ‘yan takara, kuma tana kula da ingancin zaɓe. Jagora yana naɗa limamai 6, sannan sauran 6 masu ilimin doka ne daga bangaren shari’a da majalisa ke amincewa dasu.

KU KUMA KARANTA: Ministan tsaron Saudiyya ya gana da shugaban addini na Iran Khamenei, ya miƙa masa wasiƙar Sarki Salman

Ga bayanan wanda aka naɗa ɗin:

Alireza Arafi, Shugaban makarantu na addini (Hawzah) a Iran da limamin Jumma’a na Qom.

Ahmad Khatami, Limamin Jumma’a na Tehran wanda ke wakiltar Kerman a Majalisar Masana.

Ahmad Hosseini-Khorasani, Malami daga Qom mai ƙwarewa wajen haɗa ilimin addini da tsarin doka, wakilin Razavi Khorasan a Majalisar Masana.

Jagoran ya bayyana cewa sake naɗin yana da nufin dorewar tsarin da ke kare tsarin mulkin Musulunci a Iran.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...