Connect with us

Labarai

El-Rufa’i ya rushe asibiti, makarantu da gidajen jama’a ƙasa da sati ɗaya ya bar mulki

Published

on

Da misalin karfe 1:30 na daren ranar Lahadi 21 ga watan Mayun 2023, tawagar hukumar tsara birane ta jihar Kaduna, wato KASUPDA ta rushe asibitin Kauthar da aka gina domin al’umma da makarantun Fudiyya dake Rimi, Danmadami, Tudun Wada, da gidan Alhaji Musa Birnin Yero da kuma gidan Alhaji Sulaiman Bala. Sun yi wannan ɗanyen aiki ne bisa umarnin gwamna mai barin gado Nasiru El-Rufai.

Wasu ganau sun shaidawa wakilinmu cewa jami’an rushe muhallan sun tattake Alƙur’ani mai girma tare da rushe gine-ginen kan Alƙur’anan.

KASUPDA ba su bayar da wata sanarwa ko raba wata takarda na dalilin rushe muhallan ba kamar yadda Muhammad Rabiu ya shaidawa wakilinmu a Kaduna.

KU KUMA KARANTA: Zan ci gaba da korar ma’aikata, da rushe gine-gine har zuwa rana ta ƙarshe a ofis – El-Rura’i

Idan ba ku manta ba, kafafen watsa labaran Nijeriya sun labarto cewa gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya amince da rushe muhallan waɗanda ya kira da ‘IMN’ amma shi yana muhallan nufin mabiya Shaikh Zakzaky da kuma wasu gine-gine dake Gbagyi da waɗansu wurare duk a jihar ta Kaduna ƙasa da mako biyu ya kammala mulkinsa a jihar ta Kaduna.

El-Rufai ya amince da rushe waɗannan muhallai ne a wata takarda mai ɗauke da kwanan watan 20 ga Afrilun 2023. Inda hukumar KASUPDA ke neman Naira 29,253,500 da kuma jami’an tsaro sama da dubu biyu domin gudanar da wannan aikin rushe-rushen.

Cikin adadin wannan kuɗin, hukumar ta KASUPDA na da buƙatar Naira miliyan 20,253,500 domin rushe muhallan da ya kira na ‘IMN’.

Sai dai a wata takardar ƙarar da aka shigar a gaban babbar kotun Kaduna mai ɗauke da lamba KDH/KAD/515/23; makarantun Imam Sadiq Academy LTD, Tahfiz Fudiyyah Zaria, Fudiyyah Nursery and Primary Schools., Saminu Kusa Muhammed, Ahmad Abubakar, Haruna Danfulani U/Mu’azu, Shuhada Foundation, a madadinsu da kuma ‘Yan Shi’a mazauna jihar Kaduna sun maka gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, Gwamnatin jihar Kaduna, Ma’aikatar Gidaje da ci gaban Birane ta jihar Kaduna, KASUPDA, da kuma Daraktan KASUPDA, Isma’il Umaru Dikko a gaban kotun ne bisa yunƙurin da suke yi na rusa musu muhallai ba bisa ƙa’ida ba da kuma sunan cewa na ‘IMN’ ne.

Masu shigar da ƙarar sun ce waɗannan muhallai ba su da alaƙa ta kusa ko ta nesa da abin da waɗanda aka maka gaban kotun suke iƙirari. Inda suka nemi kotun da ta dakatar da su.

Ƙarar wanda aka shigar a gaban babbar kotun jihar Kaduna, har wala yau ƙara neman da kotun ta bayar da umurnin hana rushe musu muhallai da sunan cewa na ‘IMN’ ne. Inda suka ce gine-ginensu ne da suka gina bisa ƙa’idar doka, kuma suna da dukkanin wani shaida na yin gini a jihar ta Kaduna.

Sannan sun kuma nemi kotun da ta ci tarar waɗanda ake ƙara inda aka same su da wannan laifi bisa wannan yunƙuri da suka yi na rusa musu muhallai.

Wakilinmu ya shaidi shaidar shigar da ƙarar wacce aka gabatar a gaban babbar kotun na Kaduna ɗauke da kwanan wata 18 ga watan Mayun 2023.

El-Rufai ya yi alwashin zai ci gaba da rushe-rushe da korar ma’aikata har zuwa ranarsa ta ƙarshe a ofis.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: El-Rufai ya kori sarakuna biyu da hakimai uku, a ƙasa da sati ɗaya ya bar mulki | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Gwamna Zulum ya kai ziyarar bazata a asibitin Gwoza, ya yi takaicin ganin asibitin | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like