No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sarkin Kano Sanusi, ya bawa ‘yan kasuwar waya da iftila’in gobara ta shafa tallafin Naira miliyan 10

Daga Jameel Lawan Yakasai

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi ll ya baiwa ƴan kasuwar waya ta Farm Centre tallafin Naira miliyan 10 sakamakon gobara da ta ƙone shaguna da rumfuna 47 a kasuwar a jiya Juma’a.

Sarkin ya bayyana wannan tallafi ne yayin da ya kai ziyarar nake ga kasuwar, inda ya shawarci su buɗe asusun tallafi don farfaɗo da sashen da ya kone a kasuwar, lamarin da ya haifar da nasara dukiya ta miliyoyin Naira.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta ƙone shaguna 47 a kasuwar waya ta a Kano

A cewar Sarki Sanusi, ya bada tallafin kuma ya na kira ga waɗanda abun ya shafa da su buɗe asusun tallafi su kuma aikewa duk wanda ya ke kasuwar.

Ya kara da cewa nan gaba kadan za a tara makudan kudade da za su isa a gyara kasuwar, su kuma yan kasuwa su rage asara.

Sarki Sanusi ya kuma yi addu’ar Allah Ya kiyaye faruwar gobarar nan gaba, inda ya yi wa wadanda lamarin ya shafa addu’ar Allah Ya kawo musu ɗauki.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...