No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar sojin Isra’ila ta amince da yarjejeniyar musayar waɗanda aka yi garkuwa da su da kuma tsagaita wuta na wucin-gadi da ƙungiyar Falasɗinawa ta Hamas a Zirin Gaza, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na cikin gida suka ruwaito a ranar Talata.

“Rundunar soji na shirin yin amfani da tsagaita wuta domin sake shirya dakarunta a shirye-shiryen faɗaɗa kai hare-haren ta ƙasa zuwa kudancin Gaza,” a cewar kafar yaɗa labarai ta KAN.

A cewar kafar yaɗa labaran, yarjejeniyar da aka cimma ta haɗa da tsagaita wuta na kwanaki huɗu, da kuma sakin wasu ‘yan Isra’ila 50 da Hamas ke garkuwa a musayar Falasɗinawa 150 da ke gidajen yarin Isra’ila.

Isra’ila ta yi ƙiyasin cewa aƙalla Isra’ilawa 239 ne Hamas ke tsare da su bayan harin da aka kai kan iyaka a ranar 7 ga watan Oktoba.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta yi luguden wuta a asitibin Indonesia da ke arewacin Gaza, ta kashe mutane da dama

Isra’ila ta kai hare-hare ta sama da ta ƙasa a Zirin Gaza bayan harin ba-zata na Hamas, inda ta kashe Falasɗinawa sama da 14,128, ciki har da yara 5,840 da mata 3,920, a cewar hukumomin lafiya a yankin.

Dubban gine-gine, da suka haɗa da asibitoci da masallatai da majami’u aka rusa ko lalata a hare-haren da Isra’ila ta kai ta sama da ta ƙasa kan yankin da aka yi wa awanya.

Adadin waɗanda suka mutu a Isra’ila, ya kai kusan 1,200, a cewar alkaluman hukuma.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...