No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sanarwar da mai magana da yawun kamfanin, Olufemi Soneye ya fitar tace, an warware matsalar.
Babban kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL, ya bayyana cewar matsalolin tsare-tsare ne suka sabbaba dawowar dogayen layukan mai a wasu sassan ƙasar.

Sai dai sanarwar da mai magana da yawun kamfanin, Olufemi Soneye ya fitar tace, an warware matsalar.

KU KUMA KARANTA:NNPC ta ƙara farashin man fetur a Najeriya

Sanarwar tace, “babban kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL, na so ya bayyana cewar matsalolin tsare-tsare ne suka sabbaba matsalar ƙarancin man fetur da ake fama a wasu sassan ƙasar nan a halin yanzu, kuma an riga an magance ta.

“Kuma kamfanin yana son jaddada cewar farashin albarkatun man fetur na nan a yadda suke ba su sauya ba.”

Don haka NNPCL na ƙira ga ‘yan Najeriya da su kaucewa ɗabi’ar ɓoye man, kasancewar akwai wadatarsa a ƙasar”.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...