Connect with us

Wasanni

Najeriya ta lallasa Kamaru da ci biyu da nema a gasar cin kofin Afirka

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Tawagar ƙwallon ƙafa ta Najeriya ta kai zagayen daf da na kusa da na ƙarshe, bayan da ta doke Kamaru 2-0 a wasan zagaye na biyu a gasar kofin Afirka.

Tun kan a tafi hutun rabin lokaci, Super Eagles ta ci ƙwallon farko ta hannun Ademola Lookman, kafin nan an soke wadda Semi Ajayi ya fara cin Kamaru.

Bayan da suka yi hutu ne suka koma zagaye na biyu Kamaru ta yi ta ƙoƙarin farke ƙwallon da aka zura mata, amma ba ta samu dama da yawa ba.

Daf da za a tashi daga karawar ce Super Eagles ta ƙara na biyu ta hannun Ademola Lookman, hakan ya sa tawagarta kai zagayen quarter finals.

Da wannan sakamakon Najeriya za ta fafata a zagayen daf da na kusa da na ƙarshe da Angola ranar Juma’a 2 ga watan Fabrairu.

Gabanin fafatawar Najeriya da Kamarun a ranar Asabar, Angola ta doke Namibia 3-0 a wasan farko a zagaye na biyu a wasannin da ake buga wa a Ivory Coast.

KU KUMA KARANTA: An dakatar da ‘yar tseren Najeriya Nwokocha daga wasanni kan amfani da haramtattun ƙwayoyi

Najeriya mai kofin Afirka uku jimilla ta yi nasara a kan Kamaru karo na uku a babbar gasar tamaula ta Afirka da suka haɗu a bayan nan.

Super Eagles ta yi nasara a kan Indomitable Lions a zagayen quarter finals a 2004 da aka yi a Tunisia, sannan Najeriya ta doke Kamaru 3-2 a wasannin da aka gudanar a Masar a 2019.

Najeriya ta kawo matakin zagaye na biyu a Ivory Coast, bayan da ta yi ta biyu a rukunin farko da maki bakwai, iri ɗaya da na Equatorial Guinea, wadda ta yi ta ɗaya.

Super Eagles ta haɗa maki bakwai ne, bayan tashi 1-1 da Equatorial Guinea a wasan farko a rukuni na ɗaya da cin Ivory Coast 1-0 da kuma nasara a kan Guinea – Bissau 1-0.

Ita kuwa Indomitable Lions ta yi ta biyu ne a rukuni na uku, bayan da ta yi 1-1 da Guinea da rashin nasara 3-1 a hannun Senegal, sannan ta doke Gambia 3-2.

Kamaru mai Afcon biyar ta fara da lashe kofin Afirka a kan Najeriya a 1984 da cin 3-1 da kuma 1988 da ta yi nasarar cin 1-0 da kuma a 2000 da suka tashi 2-2, Kamaru ta lashe kofin a bugun fenariti 4-3 a Afirka ta Kudu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Nishadi

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Published

on

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Sadiya Haruna ta sake aure karo na 10

Jarumar TikTok, Sayyada Sadiya Haruna ta sake amarcewa a ranar Juma’a watanni kaɗan da mutuwar aurenta da jarumin TikTok Al Ameen G-Fresh.

A wani kati da ta wallafa a shafinta na Instagram, Sadiya ta bayyana sunan angon nata a matsayin Hon. Babagana Audu Grema.

An daura auren ne da misalin ƙarfe ɗaya bayan sallar Juma’a kamar yadda katin ya nuna a birnin Maiduguri da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin tarayya ta bai wa Rahama Sadau muƙami

Auren na zuwa mako guda bayan da jarumar ta TikTok ta bayyana a shirin tattaunawa na jarumar Kannywood Hadiza Gabon “Gabon Talk Show” inda Sadiya ta caccaki G-Fresh tare da bayyana matsalolin da suka kai ga mutuwar aurenta da shi.

Auren har ila yau na zuwa ne kwana guda bayan da shirin na Gabon ya watsa tattaunawar mayar da martani da G-Fresh inda shi ma ya yi ta sukar tsohuwar matar tasa – mafi aksarin lokuta a kaikaice.

Continue Reading

Kasashen Waje

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Published

on

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

COPA America: Panama ta yi nasara kan Amurka

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta yi Allah wadai da kalaman nuna wariyar launin fata ga ‘yan wasanta a ranar Alhamis, bayan da Panama ta yi nasara a kan Amurka da ci 2-1 a gasar cin kofin Copa America.

A wani saƙo da ta wallafa a shafin X, hukumar ƙwallon ƙafa ta Amurka ta ce “Babu shakka, babu wuri a cikin wasa na irin wannan halayya ta nuna ƙiyayya da wariya.”

Sanarwar ta ƙara da cewa “Waɗannan ayyukan ba kawai ba za’a amince da su ba ne, amma kuma sun saɓa wa kimar mutuntawa da haɗa kai da muka ɗauka a matsayin hukuma.”

KU KUMA KARANTA:Manchester City ta lashe Firimiyar Ingila sau huɗu a jere

Timothy Weah, wanda baƙar fata ne, yana ɗaya daga cikin ‘yan wasan da aka ci zarafin su. An bai wa ɗan wasan gaba na Amurka jan kati kai tsaye a minti na 18 da fara wasa, saboda hannu da ya sa ya bugi ɗan wasan Panama a bayan kan sa a lokacin da ƙwallon ta fita wajen filin wasa.

Ɗan wasan Amurka Folarin Balogun ya zura ƙwallo a minti na 22 da fara wasan bayan an bai wa Weah jan kati kafin ɗan wasan Panama Blackman ya farke a minti na 26.

Fajardo ya zura ƙwallo da ta bai wa Panama nasara da ci 2-1 a minti na 83.

Weah ya fitar da wata sanarwa ta kafafan sada zumunta, inda ya bayar da haƙuri tare da neman gafarar waɗanda ya ɓata wa rai.

Yanzu haka dai Amurka, wacce ita ce ke karɓar baƙuncin gasar cin kofin na Copa America, muddin tana son zuwa zagaye na gaba to dole ne ta yi nasara a wasanta da Uruguay da zura ƙwallaye wanda ko da Panama ta yi nasara kan Bolivia za ta samu tsallake wa.

Continue Reading

Wasanni

Yalon kati ya hana Slovenia hawa mataki na biyu a guruf ɗin gasar Euro 2024

Published

on

Yalon kati ya hana Slovenia hawa mataki na biyu a guruf ɗin gasar Euro 2024

Yalon kati ya hana Slovenia hawa mataki na biyu a guruf ɗin gasar Euro 2024

Yayin da ake kammala zagayen matakin guruf-guruf a gasar Euro 2024 da ke gudana a ƙasar Jamus, a Rukunin C, ƙasashen Slovenia da Denmark sun yi kankankan a yawan maki da yawan ƙwallaye, inda duka suka ƙare da maki uku.

A rukunin nasu, Ingila ce ta zo ta farko da maki 5 bayan ta ci wasa ɗaya kuma ta yi canjaras sau biyu. Sai Serbia da ta zo ta ƙarshe da maki biyu, bayan ta yi canjaras sau biyu da rashin nasara sau ɗaya.

Sai dai ba a iya tantance wace ƙasa ce ta biyu ba a rukunin, kasancewar Denmark da Slovenia kowannensu yana da maki uku, bayan yin canjaras sau uku. Ko da aka duba yawan ƙwallayen da kowa ya ci da waɗanda aka ci shi, ƙasashen sun kuma yin arba.

Wannan ne ya tilasta wa hukumar ƙwallon ƙafa ta Turai, UEFA yin amfani da wata dokar da ba a saba jin ta ba, don fayyace waye yake mataki na biyu, don a san da wa zai kara a matakin gaba na ‘yan-16.

KU KUMA KARANTA: Manchester City ta lashe Firimiyar Ingila sau huɗu a jere

Sakamakon haka ne, aka duba wace tawaga ce ta fi ladabi, inda aka duba yawan katin gargaɗi da aka bai wa kowace ƙasa cikin wasanni uku da suka buga. Sai dai an kuma samun yawan katin nasu shi ma daidai ne.

A nan ne UEFA ta duba cewa cikin yalon katunan da aka bai wa tawagar Slovenia, akwai ɗaya da aka bai wa mataimakin kocinsu, Novakovic Milivoje, wanda ya sa aka yanke hukuncin cewa hakan ya nuna Denmark sun fi Slovenia nuna ladabi.

Wannan ne ya ba wa ƙasar Denmark dama ta samu haye wa gaban Slovenia inda ta zamo a mataki na biyu a rukunin, kuma ta tsallaka zuwa matakin siri-ɗaya-ƙwale kai-tsaye.

Amma kuma duk da cewa Slovenia ta ƙare a mataki na uku, ta samu cancantar wucewa matakin na gaba, wanda shi ne karon farko da ta kai irin wannan mataki a wata babbar gasa, a tarihin ƙasar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like