No menu items!

Sample Page Title

Date:

Mun tafka mummunar asara – ’Yan kasuwa

’Yan kasuwar Monday Market da sauransu a Maiduguri sun tafka mummunar asara sakamakon ambaliya bayan fashewar Madatsar Ruwa ta Alau mai nisan kilomita 10 daga garin.

Ranar Litinin da tsakar dare ambaliyar ta yunkuro, inda ta raba dubban mazauna unguwannin Post Office, Gwange, Moromoro, Gadar Customs, Gidan Zoo, Bulabullin, Maidoki  Roundabout, Jami’ar Maiduguri, Cocin Saint Patrick da sauaransu da muhallansu.

Wani ɗan kasuwa ya ce, “Duk shagunan da ke Monday Market da Post Office ruwa ya shanye su.”

Wasu daga cikinsu sun nuna matukar kaɗuwarsu da kuma tunanin yiyuwar maye gurbin abin da suka rasa a ambaliyar.

Wani mai sayar da sukari da fulawa a kasuwar, Muhammad Bulama, ya ce ambaliyar ta shanye kasuwar gaba ɗaya.

KU KUMA KARANTA: Ambaliyar ruwa a Maiduguri ta shafe wasu sassan garin (Bidiyo)

“Duk shagunanmu da ke kallon gidan Marigayi Alhaji Mai Sugar sun yi ambaliya, sukari da fulawa da shinkafa da kayan girki na miliyoyin Naira sun lalace.

“A sa mu a add’ua! Buhunan kayan abinci irin su sukari da shinkafa da gishiri da taliya da sauransu duk sun jike sun narke,” in ji shi.

Wakilinmu ya lura yawan ruwan da ke ambaliyar yana ƙara karuwa inda yake ƙara shiga wasu unguwanni.

Hakazalika ambaliya ta mamaye Gidan Zoo na Kyarimi ta wuce da namun dajin da ke ciki, inda a halin da ake ciki namun dajin suke neman mafaka.

Wani mazaunin yankin ya ce, “yanzu haka mun fice daga unugwar saboda gudun hari daga namun daji da kwarin da ke gidan zoo.

Rundunar ’yan sanda a Jihar Borno ta buƙaci jama’a da su ƙaurace wa yankunan da aka samu ambabaliya zuwa wasu wurare masu aminci.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...