Ƙasashen Waje
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya ya gana da Haniyeh, jagoran siyasa na Hamas, kan tsagaita wuta a Gaza
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan ya gana da shugaban ɓangaren siyasa na ƙungiyar Hamas, Ismail Haniyeh, a cewar wasu majiyoyi na diflomasiyyar Turkiyya.
Fidan and Haniyeh sun tattauna ranar Asabar kan batun tsagaita wuta nan-take a Gaza da kai ƙarin kayan agaji yankin da sakin mutanen da aka yi garkuwa da su da kuma samar da ƙasashe biyu masu ‘yancin kansu.
Hare-haren da Isra’ila take kai wa a Gaza sun raba kashi 85 na mutanen yankin da muhallansu a yayin da ake cikin tsananin rashin abinci da ruwa mai tsafta da magunguna, sannan an rusa kashi 60 na gine-ginen yankin, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya.
A watan Oktoban da ya wuce, Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya tattauna da Haniyeh bayan Isra’ila ta kaddamar da hare-hare a Gaza inda ya tabbatar masa cewa Ankara zai kai kayan agaji Gaza sannan za a ɗauko waɗanda suka jikkata a yankin domin kawo su Turkiyya su yi jinya idan akwai buƙatar hakan.
KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe farar hula bakwai a Gaza da Khan Younis
Shugaba Erdogan ya jaddada cewa ba za a samu dauwamammen zaman lafiya a yankin ba sai Falasɗinawa sun samu kasa mai zaman kanta kamar yadda take a 1967 wacce Birnin Kudus zai zama babban birninta.
Erdogan ya ƙara da cewa Turkiyya za ta ci gaba da fafutuka domin ganin an samu zaman lafiya a yankin.
Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare babu kakkautawa ta sama da ta ƙasa a Gaza tun bayan da Hamas ta kai mata barin ba-zata, wanda Tel Aviv ya ce ya kashe aƙalla mutum 1,200.
Ta kashe Falasɗinawa aƙalla 24,927, galibinsu mata da ƙananan yara, sannan an jikkata mutum 62,388, a cewar hukumar lafiya ta Falasɗinu.
Ƙasashen Waje
Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu
Mutumin da ya fi kowa tsallake haɗari a duniya ya mutu
Daga Ibraheem El-Tafseer
Frane Selak ya kasance wanda ya fi kowa tsallake rijiya da baya a duniya.
A shekarar 1962 ya tsallake haɗarin jirgin ƙasa wanda mutane 17 suka mutu, a 1963 jirgi ya faɗi da shi kowa ya mutu sai shi kaɗai ko ƙwarzane bai yi ba.
A shekarar 1966 motar safa ta lume da su a rafi mutum huɗu sun mutu amma Frane bai samu ko ƙwarzane ba a yayin da a shekarar 1973 motarsa ta kama da wuta ya tsallake rijiya da baya, ya kuma tsallake haɗarin taho mu gama da mota ta yi da shi ya tsira ya kuma lashe yuro dubu ɗari takwas a Caca a shekarar 2003.
KU KUMA KARANTA: Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki
Ƙasashen Waje
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza
Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a kudancin Gaza, inda ta tilasta wa ɗaruruwan Falasɗinawa tserewa bayan da soji suka kuma ba da umarnin ƙaurace wasu yankuna masu yawan jama’a.
KU KUMA KARANTA: Sojojin Isra’ila sun ce an yi musayar wuta da dakarun Masar
Waɗanda suka shaida lamarin sun ce an kai hari da dama a ciki da wajen birnin Khan Younis, inda aka hallaka mutane takwas kuma mutane sama da 30 suka samu raunuka, cewar wata majiyar lafiya da kuma ƙungiyar Red Crescent ta Falasɗinawa.
Ƙasashen Waje
Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC
Farashin man fetur zai ƙaru a watan Yuli a Ghana – COPEC
Ƙungiyar Kare Haƙƙin Masu Amfani da Man Fetur a Ghana ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a samun ƙarin farashin man fetur a ƙasar a farkon watan Yulin 2024.
Ƙungiyar ta Chamber for Petroleum Consumers (COPEC) ta ce akwai alamu masu ƙarfi da ke nuna cewa farashin fetur da man dizel da gas zai ƙaru baki ɗaya a gidajen man da ke faɗin ƙasar, kamar yadda kamfanin watsa labarai na ƙasar Ghana ya ruwaito.
COPEC ɗin ta ce za a samu ƙarin farashin ne sakamakon yadda farashin Cedi ɗin a ƙasar ke ƙara karewa idan aka kwatanta da dalar Amurka.
COPEC ɗin ta yi hasashen cewa farashin man fetur ɗin wanda za a rinƙa sayarwa a gidan mai zai ƙaru da kashi 2.17 cikin 100, wanda hakan ke nufin zai ƙaru daga Cedi 14.17 zuwa Cedi 15.20 a duk lita.
Sai kuma farashin dizel ana sa ran ya ƙaru zuwa 15.21 a kowace lita ɗaya, sai kuma na gas ya koma tsakanin Cedi 13.24 zuwa Cedi 14.64 a duk kilo ɗaya.
KU KUMA KARANTA: Ɗan Ghana ya kafa tarihi na rungumar bishiyoyi a duniya
Ƙungiyar ta COPEC ta bayar da shawara ga gwamnatin Ghana da ta yi duk mai yiwuwa domin rage harajin da yake a kan gas ko kuma yin tallafi a farashinsa domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su same shi a farashi mai rahusa.
Ta kuma yi ƙira ga gwamnati da kada ta yi ƙasa a gwiwa wajen dawo da matatar mai ta Tema a kan aiki (TOR) don kaucewa ko kuma rage shigo tattacen man fetur wanda a wani lokacin ake samun gurɓatacce.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano