No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ɗaya daga cikin ministocin da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura wa Majalisar dokokin ƙasar domin tantancewa ya yanke jiki ya faɗi a zauren majalisar.

Ministan wanda ya fito daga jihar Kaduna, Balarabe Abbas Lawal ya faɗi ne a daidai lokacin da ya kammala jawabi kan tarihin rayuwa da karatunsa.

Sai dai nan da nan aka ɗaga shi kuma aka zaunar da shi a kan kujera.

Majalisar dai ta shiga zaman sirri bayan faɗuwar sa.

Tun farko a lokacin da yake jawabi, Abbas ya shaida wa majalisar cewa ya yi matuƙar murnar damar da ya samu, kuma yanayi ne da bai taɓa tsintar kansa a ciki ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...